Wani Bidiyon Nishadi ya bayyana inda aka ga Maha na son Jan Rarara amma A'isha Humaira ta hana.
https://www.tiktok.com/@m_nice_rarara/video/7546352394196520200?_t=ZS-8zY7syO4lQf&_r=1
Wannan wasu musulmai ne a kasar Amurka da suka fito suke zanga-zanga dan neman a haramta cin naman Alade da shan giya da caca
Lamarin ya farune a Texas inda abin ya matukar dauki hankula sosai wasu na cewa suna da 'yancin yin hakan wasu kuma na ganin yin hakan ganganci ne.
Kalli Bidiyonsu a kasa:
https://twitter.com/RadioGenoa/status/1964713441899565330?t=xzY6NH0Q3Rz5MgL3aZbY4A&s=19
An ga katafaren gida na Alfarma da tsohon gwamnan jihar Abia, Orji Kalu ya mallaka a Maryland dake kasar Amurka.
Lamarin ya dauki hankula sosai inda akai ta cece-kuce wasu na fadin cewa abin birgewane inda wasu kuma ke cewa ba da kudinsa ya saya ba.
https://twitter.com/ChuksEricE/status/1964690041445503097?t=QNJuC22yYEtxJ5F_MOYxzQ&s=19
Hukumar 'yansandan Najeriya ta garagadi Mutane da cewa, baiwa 'yansandan Najeriya kudi ko cin hanci a yayin da suke bakin aiki shima laifi ne.
Hukumar ta gargadi 'yan Najeriya da su yi hankali su daina daukewa 'yansandan hankali daga aikin da suke.
Sanarwar ta fito ne daga bakin hukumar 'yansandan babban birnin tarayya Abuja.
https://twitter.com/FCT_PoliceNG/status/1964752773083181153?t=Hw13v97hldjZVynO-RQ3Lg&s=19
Ministan Kwadago, Muhammadu Dingyadi ya kira Kungiyar ma'aikatan man fetur ta kasa, NUPENG da kuma kamfanin matatar man Dangote dan ya zauna dasu kan rikicin da ya bulla a tsakaninsu.
Kungiyar ta NUPENG ta zargi Dangote da yin kaka gida a harkar man fetur da rashin biyan ma'aikata da kyau da rashin baiwa ma'aikata damar shiga kungiyoyin fafutuka na ma'aikata da sauransu.
Kungiyar Tuni ta shirya shiga yajin aiki dan nuna rashin amincewa da tsare-tsaren Matatar mam fetur ta Dangote wanda tace ya sabawa ka'idar aiki wanda kuma tuni Kungiyar Kwadago ta NLC ta amince da wannan yajin aiki.
Saidai wannan kira da ministan ya musu ana sa ran dai kawo karshen lamarin.
Babban malamin addinin Islama, Sheikh Sani Yahya Jingir ya bayyana cewa, Kafurci da Munafurci ne ke sa mutane cewa ana tsanin matsalar tsaro a Najeriya.
Malam ya bayyana hakane a yayin da yake wa'azi inda yace su dai sun je jihar Kebbi sun dawo Lafiya.
Kalli Bidiyon jawabinsa:
https://www.tiktok.com/@i_am_saeed01/video/7546550346475179270?_t=ZS-8zXbRcRPa4W&_r=1
Malamin Addinin Islama, Sheikh Yusuf Sambo Rigachukun ya bayyana rashin jin dadinsa game da wa'azin Izala da aka yi a jihar Kebbi amma ba'a yi maganar matsalar tsaron yankin ba.
Malam yace mutane sun fi 100 da suka kirashi suna nuna damuwa akan Lamarin.
Malam yace kuma an yi hakane wai dan kada a batawa Gwamnati rai.
Yace suma suna tare da wasu jami'an Gwamnatin amma hakan ba zai hanasu fadar gaskiya ba.
https://www.tiktok.com/@abdullahingwandutv/video/7545975485742763284?_t=ZS-8zXZs1JmLPV&_r=1
Wannan me yin Tiktok din me suna Rukayya tace tambayarta shine an ce Maulidin Annabi(Sallallahu Alaihi Wasallam) ake yi amma kuma gashi sai kaga hotunan Inyas a jikin masu Maulidi me yasa haka?
Sannan ta yi tambayar cewa, me yasa ba za'a yi Maulidi a gida ba sai an tare hanya saboda ta fito zata je shago amma aka tare musu hanya.
Sannan tace me yasa Shehunan Darika ke yafa koren mayafi?
https://www.tiktok.com/@rukaiya_magaji/video/7547348972520754439?_t=ZS-8zXYmWviWDw&_r=1
Nafisa K. Abdullahi ta baiwa maza shawarar cewa daga yanzu duk wanda zai kara aure kar ya yadda mace ta tube yaganta tsirara.
Tace har zai iya kai hannu ma ya taba dan ya tabbbatar komai na gaskiya ne.
Ta bayyana hakane a Bidiyon data wallafa a shafinta na Tiktok inda tace cutar da akewa maza ta yi yawa.
https://www.tiktok.com/@official_feenat/video/7540546172046281990?_t=ZS-8zXXVW0zMQL&_r=1
Gwamnan jihar Kaduna, Malam Sanata Uba Sani ya musanta ikirarin cewa, Tsohon Gwamnan jihar, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai uban gidanda ne a siyasance kuma shine ya koya masa soyasa.
Ya bayyana hakane a hirar da aka yi dashi a Channels TV inda aka tambayeshi me zai ce game da ikirarin El-Rufai na cewa shine ya koya masa siyasa?
Gwamna Uba Sani yace baya son mayar da martani akan wani mutum daya dan hankalinsa na kan jihar Kaduna.
Yace amma Shugabab kasa, Bola Ahmad Tinubu da tsohon lauya, marigayi Chief Gani Fawehinmi sune iyayensa a siyasa sune suka koya masa siyasa.