Tuesday, December 16
Shadow
Kano: Shugaban ƙaramar hukumar Wudil ya ɗauki nauyin ɗalibai mata 33 su karanci ilimin ungozoma

Kano: Shugaban ƙaramar hukumar Wudil ya ɗauki nauyin ɗalibai mata 33 su karanci ilimin ungozoma

Duk Labarai
Shugabann karamar hukumar Wudil, Abba Muhammad Tukur ya ɗauki nauyin karatun ɗalibai mata 33 domin su karanci aikin ungozoma, da nufin inganta lafiyar mata masu juna-biyu a yankin. Bayan daukar nauyin karatun nasu har su kammala, Tukur ya mikawa ɗaliban takardar samun gurbin karatu ta kwalejin koyar da harkokin aikin ungozoma da ke Kano. Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da Babban Sakataren yada labaran shugaban karamar hukumar, Nura Mu'azu Wudil ya sanyawa hannu, inda ya ce qannan kuma kari ne kan ɗalibai mata 10 da tuni suka fara karatun. Sanarwar ta ce, Tukur ya duba muhimmancin ilimin ƴaƴa mata, inda ya kara da cewa, hakan ne ya sa ya ware kudade masu yawa don ba su Ilimi da kuma kawo karshen yawan samun mutuwar mata masu dauke da juna biyu. Tukur, a cewar Sakataren, ya...
Da Duminsa: Saboda munin hare-haren da aka kai jihar Benue, na dakatar da duk wani aiki da nake zan kai ziyara jihar Benue>>Shugaba Tinubu

Da Duminsa: Saboda munin hare-haren da aka kai jihar Benue, na dakatar da duk wani aiki da nake zan kai ziyara jihar Benue>>Shugaba Tinubu

Duk Labarai
Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya sanar da cewa ya dakatar da duk wani aiki da yake zai kai ziyara jihar Benue. Hakan na zuwane bayan da hare-haren da ake zargin fulani makiyaya da kaiwa suka yi sanadiyyar kisan sama da mutane 100 a jihar ta Benue. Zanga-zanga ta barke a jihar inda kuma aka kai jami'an tsaro na musamman. 'Yan Adawa tuni suka fara sukar shugaban kasar saboda zargin rashin nuna kulawa sosai akan lamarin. shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya bayyana cewa zai kai ziyyara jihar Benue ranar Laraba. Ya fadi hakane a ranar Litinin a lokacin da yake kaddamar da wani shirin ruwa a Abuja. Ya jawo hankalin mutanen jihar ta Benue da su kai zuciya nesa su rika hakuri da juna.
Hare-haren da ake kaiwa jihar Benue sun kai matakin da ba zamu kauda kai ba>>Atiku Abubakar

Hare-haren da ake kaiwa jihar Benue sun kai matakin da ba zamu kauda kai ba>>Atiku Abubakar

Duk Labarai
Dan takarar shugaban kasa na jam'iyyar PDP a zaben 2023, Atiku Abubakar yayi Allah wadai da hare-haren da aka kai jijar Benue. Atiku yace hare-haren sun kai matakin da ba za'a iya kauda kai ba. Yace wani abin takaici shine yanda ake harbawa masu zanga-zangar da suka fito suke nuna damuwa kan lamarin barkonin tsohuwa. Yace suna neman a basu tsaron rayuwarsu ne. Yace yana kira ga hukumomi su daina yin Allah wadai kawai su rika tashi tsaye suna daukar mataki. Yace kuma ba jihar Benue bace kadai akwai jihohin Zamfara, Katsina, Plateau, da Taraba dake fama da irin wannan matsala ta tsaro.
Mashaya giya sun yi barazanar fara zanga-zanga muddin gwamnati bata rage farashin giyar ba

Mashaya giya sun yi barazanar fara zanga-zanga muddin gwamnati bata rage farashin giyar ba

Duk Labarai
{"remix_data":[],"remix_entry_point":"challenges","source_tags":[],"origin":"unknown","total_draw_time":0,"total_draw_actions":0,"layers_used":0,"brushes_used":0,"photos_added":0,"total_editor_actions":{},"tools_used":{},"is_sticker":false,"edited_since_last_sticker_save":false,"containsFTESticker":false} Kungiyar mashaya giya a kasar Ghana sun baiwa gwamnatin kasarsu sati 3 ta sauke farashin giyar ko kuma su tsunduma zanga-zanga. Kungiyar tace membobinta Miliyan 16.65 dake fadin kasar zasu bazama zanga-zanga muddin Gwamnatin bata rage farashin giyar ba. Daya daga cikin membobin kungiyar, Moses Obuah ne ya bayyana hakan inda yace darajar kudin Ghana da ake cewa, Cedi ta karu dan haka suma suna kiran a rage musu farashin giyar dan samun saukin rayuwa. Ya koka da cewa, Abin taka...
An kai Jami’an tsaro na musamman jihar Benue bayan munanan hare-hare

An kai Jami’an tsaro na musamman jihar Benue bayan munanan hare-hare

Duk Labarai
{"remix_data":[],"remix_entry_point":"challenges","source_tags":[],"origin":"unknown","total_draw_time":0,"total_draw_actions":0,"layers_used":0,"brushes_used":0,"photos_added":0,"total_editor_actions":{},"tools_used":{},"is_sticker":false,"edited_since_last_sticker_save":false,"containsFTESticker":false} Rahotanni sun ce an kai jami'an tsaro na musamman jihar Benue bayan munanan hare-haren da suka faru a jihar. Gwamnan jihar, Hyacinth Alia ne ya bayyana hakan ta bakin kakakinsa, Mr Tersoo Kula a wata sanarwa da ya fitar ga manema labarai a Makurdi. Ya bayyana cewa yana tare mutanen jihar a takaicin da suke nunawa na harin da aka kai wanda yayi sanadiyyar kisan mutane Akalla 100. Gwamnan yace yana hada kai da jami'an tsaro na tarayya wanda yanzu haka sun kan hanyar zuwa jihar. ...
Bidiyo Da Duminsa: An gano hadimin shugaba Tinubu na munafurtarsa wajan kitsa yanda zai fadi zabe a 2027

Bidiyo Da Duminsa: An gano hadimin shugaba Tinubu na munafurtarsa wajan kitsa yanda zai fadi zabe a 2027

Duk Labarai
{"remix_data":[],"remix_entry_point":"challenges","source_tags":[],"origin":"unknown","total_draw_time":0,"total_draw_actions":0,"layers_used":0,"brushes_used":0,"photos_added":0,"total_editor_actions":{},"tools_used":{},"is_sticker":false,"edited_since_last_sticker_save":false,"containsFTESticker":false} Tsohon hadimin shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu, Aliyu Audu ya bayyana cewa dalilin da yasa ya sauka daga mukamin me baiwa shugaban kasar shawara ta musamman shine yana munafurtar shugaban kasar. Yace ba zai yiyu ya ci gaba da zama a gwamnatin Tinubu ba bayan yasan cewa, yana kitsa yanda zai fadi zabe a shekarar 2027. Aliyu ya bayyana hakane a hirar da aka yi dashi a gidan talabijin na Channels TV inda kuma ya nanata cewa lallai zasu kayar da shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu a za...
Bidiyo: Ji Tonon Silili yanda shugabar Bankin Fidelity Bank tace ta biya Naira Biliyan 5 dan kada ‘yan sanda su kamata bayan zarginta da cinye makudan kudade

Bidiyo: Ji Tonon Silili yanda shugabar Bankin Fidelity Bank tace ta biya Naira Biliyan 5 dan kada ‘yan sanda su kamata bayan zarginta da cinye makudan kudade

Duk Labarai
{"remix_data":[],"remix_entry_point":"challenges","source_tags":[],"origin":"unknown","total_draw_time":0,"total_draw_actions":0,"layers_used":0,"brushes_used":0,"photos_added":0,"total_editor_actions":{},"tools_used":{},"is_sticker":false,"edited_since_last_sticker_save":false,"containsFTESticker":false} Wani Bidiyo ya bayyana na shugabar Bankin Fidelity Bank, Onyeali-Ikpe inda take cewa ta biya Naira Biliyan 5 dan kada 'yansanda su kamata. Hakan na zuwan bayan da ake zarginta da satar ko cinye ko aikata zamba da Naira ₦19Billion. https://twitter.com/SaharaReporters/status/1934547138106786223?t=ToB34Rrj9DdOxiFVwZGjnQ&s=19 A baya ma dai an zargi wata magumagu bayan ganin an cireta daga cikin sunayen wadanda ake zargi da rashawa da cin hanci.
Najeriya na son siyo irin wadannan jiragen 12 daga kasar Amurka dan magance matsalar tsaro

Najeriya na son siyo irin wadannan jiragen 12 daga kasar Amurka dan magance matsalar tsaro

Duk Labarai
{"remix_data":[],"remix_entry_point":"challenges","source_tags":[],"origin":"unknown","total_draw_time":0,"total_draw_actions":0,"layers_used":0,"brushes_used":0,"photos_added":0,"total_editor_actions":{},"tools_used":{},"is_sticker":false,"edited_since_last_sticker_save":false,"containsFTESticker":false} Rahotanni sun ce gwamnatin tarayya na shirin siyo jiragen sama da ake kira da AH-1Z Viper attack helicopters guda 12 daga kasar Amurka. Shugaban sojojin sama, Air Marshal Hasan Abubakar, ne ya wakilci Najeriya wajan zuwa kasar Amurka dan tattauna maganar siyen jiragen. Kakakin Hukumar sojin Saman Najeriya, Air Commodore Ehimen Ejodame ne ya fitar da sanarwar inda yace an yi ganawar tsakanin shugaban sojojin Najeriya da kuma wakilan kasar Amurka a birnin San Diego na jihar Califor...
Kotu ta daure abokai biyu da suka saci kayan sawa tsawon watanni 12 a gidan yari

Kotu ta daure abokai biyu da suka saci kayan sawa tsawon watanni 12 a gidan yari

Duk Labarai
Kotu a Jos, babban birnin jihar Filato ta yankewa abokai biyu hukuncin daurin watanni 12 a gidan yari. Wadanda aka daure din sune, Michael Auta da Gabriel Sunday. Dukan su dai sun amsa laifinsu. Kayan da suka sata darajarsu ta kai Naira 488,000. Mai shari'a, Mrs Shawomi Bokkos ta yanke musu hukuncin daurin watanni 2 a gidan yari ko kuma su biya diyyar Naira 50000. Sannan ta bukaci kowannen su ya baiwa me shagon Naira 200,000 ko kuma a kara musu wani hukuncin daurin watanni 12. Dansanda me gabatar da kara, Insp Daniel Damulak ya gabatarwa da kotu cewa wata mata me suna Ms Gift Ernest ranar 17 ga watan Aprilu ya kai musu korafi. Ta yi zargin wadanda aka kama din sun shiga shagonta inda suka sace mata kayan da suka kai na Naira 488,000. Yace kuma bayan bincike duka sun...
Ana zargin “Gwamnan Gombe baya son Shugaba Tinubu yayi takara da Shettima a zaben 2027 saidai Tsoro ya hanashi fitowa ya fada”

Ana zargin “Gwamnan Gombe baya son Shugaba Tinubu yayi takara da Shettima a zaben 2027 saidai Tsoro ya hanashi fitowa ya fada”

Duk Labarai
Shiga tasharmu ta WhatsApp dan samun labarai: https://whatsapp.com/channel/0029VbA9rBN1SWt61nQZUj1g A yayin da ake dambarwa kan rade-radin canja mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima kamin zaben shekarar 2027. Rahotanni daga jaridar Vanguard na cewa, Wata majiya ta shaidawa jaridar cewa, Gwamnan Gombe, Inuwa Yahya baya son shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya ci gaba da tafiya da Kashim Shettima a matsayin mataimaki musamman a zaben shekarar 2027. Saidai Gwamnan ya kasa fitowa ya fadi abinda ke zuciyarsa saboda tsoro. Bakan na zuwa ne bayan da aka tashi Baran-Baran a taron masu ruwa da tsaki na Arewa maso gabas saboda an kira sunan shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu amma ba'a kira sunan Kashim Shettima ba. Ana zargin akwai yiyuwar shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu zai canja ...