Tuesday, December 16
Shadow
Ji Cikakken Bayani kan hadarin jirgin saman Indiya inda mutane sama da 200 suka mùtù, an bayyana kudin diyyar da kamfanin jirgin zai biya iyalan màmàtàn

Ji Cikakken Bayani kan hadarin jirgin saman Indiya inda mutane sama da 200 suka mùtù, an bayyana kudin diyyar da kamfanin jirgin zai biya iyalan màmàtàn

Duk Labarai
Wani jirgin sama mallakin kamfanin sufuri na Air Indiya ya yi hatsari inda ya faɗa kan wata unguwa da ke birnin Ahmedabad a yammacin ƙasar Indiya. Shugaban kamfanin lura da sufurin jiragen sama na Indiya ya ce akwai fasinjoji da ma'aikata 242 a cikin jirgin. Bidiyo da ake yadawa a shafukan sada zumunta ya nuna baƙin hayaƙi ya turnuƙe bayan rikitowar jirgin. Babu tabbacin adadin mutanen da suka mutu ko suka jikkata sanadiyyar hatsarin. Jirgin na kan hanyarsa ne daga Indiya zuwa Birtaniya. Ma'aikatan kashe gobara da masu bayar da agajin gaggawa sun garzaya wurin da lamarin ya faru. Akwai yiwuwar dukkanin fasinjojin jirgin Indiya da ya yi hatsari sun mutu Kamfanin dillancin labaru na AP ya ambato shugaban ƴansanda na birnin Ahmedabad na cewa akwai yiwuwar babu wanda ya ts...
Ya kamata a dawo da tallafin aikin hajji ga maniyyatan Najeriya – Ndume

Ya kamata a dawo da tallafin aikin hajji ga maniyyatan Najeriya – Ndume

Duk Labarai
Jagoran ƴan kwamitin majalisar dattijan Najeriya kan harkokin ƙasashen waje a lokacin aikin hajjin 2025, Sanata Ali Ndume ya buƙaci da a mayar da tsarin bayar da tallafi kan batun aikin hajji a ƙasar domin rage tsadar kujera ga maniyyata. Ndume ya fadi haka ne a tattaunawarsa da BBC jim kadan bayan kammala aikin hajjin 2025 a ƙasar Saudiyya. Sanatan wanda ya nuna gamsuwa kan tsarin da aka samar ga mahajjatan Najeriya a Saudiyya ya ce "dama gwamnatin da ta shuɗe ita ce ta cire tallafin da ake bayarwa kan aikin hajji, saboda haka ya kamata a dawo da bayar da tallafi saboda aikin hajjin ya yi tsada." Mahajjatan Najeriya a 2025 sun biya kuɗin kujera ne tsakanin naira miliyan 8.3 zuwa miliyan 8.8 dangane da ɓangaren ƙasar da suke zama. Hakan ya ɗara abin da maniyyatan Najeriya suka ...
Ina jin daɗin ganin jam’iyyun adawa cikin matsala – Tinubu

Ina jin daɗin ganin jam’iyyun adawa cikin matsala – Tinubu

Duk Labarai
Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya ce yana farin ciki da halin rikici da jam'iyyun adawa da dama na ƙasar ke ciki. Shugaban ya bayyana haka ne a lokacin jawabin da ya yi na ranar tunawa da dimokuraɗiyya a zauren majalisar dokokin ƙasar da ke Abuja, yau Alhamis. "Ina jin daɗin ganin jam'iyyun adawa a tagayyare," kamar yadda shugaban ƙasar ya bayyana a jawabinsa na ranar dimokuraɗiyya. Tinubu ya ce "ba zan ce ina so na ga kun gyaru ba, ina ma jin dadin ganin ku a haka. Hakan na zuwa ne yayin da jam'iyyar APC mai mulkin ƙasar ke ci gaba da karɓar ƴan siyasa masu sauya sheƙa daga jam'iyyun adawa zuwa cikinta. Tinubu ya ce jam'iyyar APC ba za ta hana kowa shiga cikinta ba domin yin hakan tauye hakkin al'umma ne.
Kungiyar dake saka ido kan makamin kare dangi ta Duniya tace kasar Ìràn ta munafurceta ta hanyar kin bayyana mata shirin da take na mallakar makamin

Kungiyar dake saka ido kan makamin kare dangi ta Duniya tace kasar Ìràn ta munafurceta ta hanyar kin bayyana mata shirin da take na mallakar makamin

Duk Labarai
{"remix_data":[],"remix_entry_point":"challenges","source_tags":[],"origin":"unknown","total_draw_time":0,"total_draw_actions":0,"layers_used":0,"brushes_used":0,"photos_added":0,"total_editor_actions":{},"tools_used":{},"is_sticker":false,"edited_since_last_sticker_save":false,"containsFTESticker":false} Hukumar Majalisar Ɗinkin Duniya da ke sanya ido kan mnakaman nukiliya ta yanke hukuncin cewa Iran ta karya ƙa'ida da aka shimfiɗa kan makaman Nukuliya. Bayan an kaɗa ƙuri'ar makamai a Vienna, hukumar ta kuma nemi Iran ta yi bayanin yadda aka gano kayan haɗa makaman nukiliya a wasu yankuna da Tehran ba ta bayyana ba. Daukar sabon matakin zai iya kaiwa ga sabbin takunkuman da aka janyewa ƙasar shekaru 10 da suka gabata. Da Iran take mayar da martani ta ce, sakamakon hukumar cike...
APC ta zargi Gwamnatin Kano da ciyo bashin Dala Miliyan 6.6 daga ƙasar waje tare da neman bahasin yadda aka yi da kuɗaɗen

APC ta zargi Gwamnatin Kano da ciyo bashin Dala Miliyan 6.6 daga ƙasar waje tare da neman bahasin yadda aka yi da kuɗaɗen

Duk Labarai
APC ta zargi Gwamnatin Kano da ciyo bashin Dala Miliyan 6.6 daga ƙasar waje tare da neman bahasin yadda aka yi da kuɗaɗen Wata ƙungiya a cikin jam’iyyar APC a jihar Kano mai suna APC Patriotic Volunteers ta zargi gwamnatin jihar da karɓar bashi daga ƙasashen waje har Dala Miliyan 6.6 ba tare da bayyana inda kuɗaɗen suka tafi ba. Shugaban ƙungiyar na ƙasa, Alhaji Usman Alhaji ne ya yi wannan zargi a taron manema labarai da aka gudanar a Kano a yau Laraba. Jaridar DAILY NIGERIAN ta rawaito cewa taron manema labaran an shirya shi ne domin nazarin ayyukan gwamnatin jam’iyyar NNPP a Kano cikin shekaru biyun da ta yi a kan mulki. A cewar Alhaji Usman, ƙungiyar na da hujjoji daga Ofishin Kula da Lamuran Bashi na Ƙasa (DMO) da ke nuna cewa gwamnatin Gwamna Abba Kabir Yusuf ta karɓi bas...
Yarbawan Arewa sun yiwa shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu alkawarin Kuri’u Miliyan 10 a zaben 2027

Yarbawan Arewa sun yiwa shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu alkawarin Kuri’u Miliyan 10 a zaben 2027

Duk Labarai
Kungiyar yarbawa magoya bayan shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu me suna (NOYAT) sun yiwa shugaban kasar Alkawarin samar masa da kuri'u Miliyan 10. Kungiyar a shekara 2022 ta shirya taro na musaman kan goyon bayan shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu a jihar Kaduna wanda ya samu halartar manyan mutane ciki hadda malaman addini. A sanarwar da kungiyar ta fitar ranar Laraba, ta sanar da cewa, tana jinjinawa shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu saboda nada Yazeed Shehu Danfulani shugaban hukumar inshora ta manoma ta kasa, (NAIC). Kungiyar a sanarwar wadda kakakinta, Mr. Seun Ogunyinka ya ftar tace nadin ya karfafa matasa sannan kuma 'yan Najeriya da dama sun ji dadi inda suka bayyana Danfulani a matsayin gwarzo wanda aka sanshi da aiki Tukuru.
Dukkan Alamu na nuni da cewa, kasar Amurka da Israyla na gaf da afkawa kasar Ìràn da yaki, Amurkar ta fara kwashe ‘yan kasarta daga ofisoshin jakadancin dake gabas ta tsakiya

Dukkan Alamu na nuni da cewa, kasar Amurka da Israyla na gaf da afkawa kasar Ìràn da yaki, Amurkar ta fara kwashe ‘yan kasarta daga ofisoshin jakadancin dake gabas ta tsakiya

Duk Labarai
Kasar Amurka ta bayar da umarnin kwashe ma'aikatan ta dake ofishin jakadancinta na kasar Iraqi inda ta bayyana cewa akwai fargabar tsaro. Hakanan rahotanni sun ce Amurkar ta na kwashe wakilanta daga kasar UAE Ana tsammanin haka shirine na Afkawa kasar Ìràn da yaki saboda hanata mallakar makamin kare dangi. Kasar Iran tace muddin Amurka ko Israyla suka kai mata hari, zata tabbatar ta kaiwa kadarorin kasar Amurkar dake yankin Gabas ta tsakiya hari. Shugaban Amurka, Donald Trump ya bayyana cewa, ba zasu bar Iran ta mallaki makamin kare dangi ba. Rahotanni sun ce kasar Iran ta ki baiwa Amurka hadin kai a tattaunawar neman sulhu dan karta mallaki makamin kare dangi.
Masu zanga-zanga sun shirya tsaf dan nunawa shugban kasa, Bola Ahmad Tinubu fushinsu a yau ranar Dimokradiyya

Masu zanga-zanga sun shirya tsaf dan nunawa shugban kasa, Bola Ahmad Tinubu fushinsu a yau ranar Dimokradiyya

Duk Labarai
Rahotanni sunce akwai artabu da dauki ba dadi da akw tsammanin zau faru a yau tsaanin masu zanga-zanga da jami'an tsaro a majalisar tarayya dake Abuja. Masu zanga-zangar ta ranar 'yanci shin shirya zanga-zangar a Abuja dama gurare 19 a fadin kasarnan. A yau ne ake sa ran shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu zai halarci majalisar tarayya dan karrama wasu 'yan majalisar sannan a canne zai gabatarwa da 'yan kasa jawabi. A baya dai, shugaban kasar ya so ya gabatar da jawabin ga 'yan kasa da safiyar Ranar Alhamis amma daga baya aka canja tsari aka ce sai ya je majalisar tarayya. Maau zanga-zangar sun ce zasu gabatar da kokensu ne game da matsalar matsim tattalin arzikin da talakawa ke ciki.
Karanta Jadawalin manyan gurare 7 da aka sakawa sunan shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu tun bayan da ya hau mulki

Karanta Jadawalin manyan gurare 7 da aka sakawa sunan shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu tun bayan da ya hau mulki

Duk Labarai
Tun daga 29 ga watan Mayu na shekarar 2023 bayan da shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya zama shugaban Najeriya, an sakawa manyan gurare na gwamnati guda 7 sunansa. Daga cikin abubuwan da aka sakawa sunan Shugaban kasar akwai tituna, Barikin sojoji, dakunan taro da sauransu. Wata kungiyar rajin kare hakkin bil'adama me suna (NEFGAD) ta bayyana hakan a matsayin abinda bai dace ba dan ya sabawa aikin gwamnati. Ga jadawalin gurare 7 da aka sakawa sunan shugaban kasar kamar haka: Babban Filin Jirgin sama na jihar Naija. A ranar March 10, 2024 ne gwamnan jihar Naija, Umar Bago ya sakawa babban filin sauka da tashin jiragen jihar dake Minna sunan shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu. Titun Abuja Southern Parkway. A ranar May 28, 2024 ne bayan kammala titin Abuja Southern Parkway...