Monday, December 15
Shadow
Ji Dalilin da yasa shugaba ‘yan siyasa ke ta tururuwa zuwa gidan Tinubu dake Legas

Ji Dalilin da yasa shugaba ‘yan siyasa ke ta tururuwa zuwa gidan Tinubu dake Legas

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa gidan Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu dake Legas ya zama kamar wata makkar 'yan siyasa. Inda suke ta tururuwa dan zuwa ganinsa tun bayan da ya fara hutun Sallah a can. Tinubu ya je Legas ranar 27 ga watan Mayu inda ya halarci taron kungiyar ECOWAS sannan daga nan ya kaddamar da wasu ayyuka sannan ya fara hutun Sallah. Daga cikin manyan 'yan siyasar da suka kaiwa shugaba Tinubu ziyara akwai; Gwamnan jihar Filato, Caleb Muftwang. Fasto Tunde Bakare. Dakataccen gwamnan jihar Rivers, Simi Fubara. Gwamnan jihar Osun, Senator Ademola Adeleke. Sai kuma Ministan kasafin Kudi, Atiku Bagudu. masana dai sun ce ganin Tinubu a Legas yafi sauki fiye da ganinsa a Abuja, sannan da maganar zaben 2027 na daga cikin dalilan da 'yan siyasr ke ta tururuwa...
Najeriya tazo ta uku a jerin kasashe mafiya yawan masana’antu a Nahiyar Afrika

Najeriya tazo ta uku a jerin kasashe mafiya yawan masana’antu a Nahiyar Afrika

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa Najeriya ta zo ta 3 a jerin kasashe 10 mafiya yawan masana'antu a Nahiyar Afrika. Kafar The African Exponent ce ta wallafa wannan bayani. Kafar tace ta yi binciken nata ne aka shekaru 10 da suka gabata inda ta bayar da muhimmanci ga kasashen dake da masana'antu mafiya yawa dake samar da abubuwan amfani. Jadawalin kasashen sune kamar haka: South Africa; Egypt; Nigeria; Morocco; Kenya; Algeria; Ethiopia; Ghana; Tunisia; and Zambia.
Bayan Allah sai Tinubu a gurina, dan ko iyalina, da mahaifana basu kaimun Tinubu ba>>Inji Ministan Ayyuka, David Umahi

Bayan Allah sai Tinubu a gurina, dan ko iyalina, da mahaifana basu kaimun Tinubu ba>>Inji Ministan Ayyuka, David Umahi

Duk Labarai
Ministan Ayyuka, David Umahi ya bayyana cewa, bayan Allah sai Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu a wajensa. Ya bayyana hakane a yayin ganawa da manema labarai a Abakaliki yayin da yake bayyana irin jinjina da amincin da shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya bashi. Yace yabon da shugabab kasa, Bola Ahmad Tinubu ya masa yafi mai a bashi Dala Tiriliyan daya. Yace kuma a kullun yana fada idan har ya dora iyalinsa ko danginsa a sama da Allah ko Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu to kada Allah ya biya masa bukatunsa.
Yawan ‘yan majalisar APC ya karu a majalisar tarayya bayan canja sheka da ‘yan PDP da Labour  party da NNPP suka yi ta yi

Yawan ‘yan majalisar APC ya karu a majalisar tarayya bayan canja sheka da ‘yan PDP da Labour party da NNPP suka yi ta yi

Duk Labarai
Yawan 'yan majalisar Jam'iyyar APC a majalisar tarayya ya karu bayan da 'yan jam'iyyar Hamayya suka rika canja sheka kamar farin dango. A yanzu yawan 'yan majalisar dattijai na jam'iyyar APC sun karu zuwa 68 a yayin da yawan 'yan majalisar wakilanta suka karu zuwa 207. Hakan na zuwane yayin da majalisar ta 10 ta cika shekaru 2 da kafuwa. Idan rahotannin dake cewa sanata Senator Neda Imasuen daga jihar Edo dan jam'iyyar Labour party zai canja sheka zuwa jam'iyyar APC suka tabbata, to yawan 'yan majalisar Dattijai na jam'iyyar zai karu zuwa 69 kenan. Hakanan yawan sanatocin APC din zasu karu idan Sanata Ahmed Wadada Aliyu daga jihar Nasarawa wanda ya bar jam'iyyar SDP ya koma jam'iyyar APC. Ana zargin jam'iyyar APC da kokarin mayar da Najeriya tsarin jam'iyya daya.
Kasar Ìràn tace idan dai Amurka na son a yi sulhu kan shirin ta na mallakar makamin kare dangi, to itace zata gindaya sharudan da za’a bi ba Amurkace zata mata katsalandan ba

Kasar Ìràn tace idan dai Amurka na son a yi sulhu kan shirin ta na mallakar makamin kare dangi, to itace zata gindaya sharudan da za’a bi ba Amurkace zata mata katsalandan ba

Duk Labarai
Kasar Iran tace bata aminta da sharudan da kasar Amurka ta gindaya mata na maganar sulhun makamin kare dangin da take son mallaka ba. Iran tace ita kasa ce me cin gashin kanta dan haka ba zata saurari Amurka ta bata sharadi akan yanda zata gudanar da kasarta ba ko makamin kare danginta ba. Iran tace idan dai ana son tattaunawar ta ci gaba, to itace zata gindaya sharudan da za'a bi wajan ci gaba da tattaunawar.
Kiris ya hana in daina karatun saboda takurar malamai>>Matar Tsohon Shugaban kasa, Patience Jonathan bayan ta kammala karatun Digiri na 3

Kiris ya hana in daina karatun saboda takurar malamai>>Matar Tsohon Shugaban kasa, Patience Jonathan bayan ta kammala karatun Digiri na 3

Duk Labarai
Matar tsohon Shugaban kasa, Patience Jonathan bayan ta kammala karatun Digiri na 3 watau PhD ta bayyana irin wahalar da ta sha. Ta bayyana hakane a wajan taron cocin Streams of Joy International Church. Tace a lokacin da ta je sayen fom din fara karatun ta rika kokwanton ko zata iya, shin me ma zata yi da wannan karatun tunda da ta zama har matar shugaban kasa? Tace amma ta karfafa kanta inda tace idan 'ya'yanta zasu iya to itama zata iya. Tace malamai idan ta kai musu aikinta sai su rika ce mata taje ta gyara guri kaza da kaza, tace hakan yana sa ta tambayi cewa shin wadannan basu san cewa ta tsufa ba? Tace a haka dai Allah ya taimaketa ta kammala karatun.
Tunubu yafi Atiku da Peter Obi wayau>>Inji Wani Me fada aji a yankin Yarbawa

Tunubu yafi Atiku da Peter Obi wayau>>Inji Wani Me fada aji a yankin Yarbawa

Duk Labarai
Wani me fana aji a yankin yarbawa wanda kuma dan PDP ne ne suna Segun Sowunmi ya bayyana cewa, shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu yafi Atiku Abubakar da Peter Obi wayau. Segun Sowunmi tsohon me magana da yawun Atiku ne wanda yace haduwarsa da Tinubu ba tana nufin ya ci Amanar Atiku bane. Yace a matsayinsa na mutum me hankali yana da 'yancin yin abinda yake so. Ya bayyana hakanne a hirar da aka yi dashi a gidan Talabijin na Channels TV duk da yake cewa a baya ya soki gwamnatin Tinubu sosai.
Kalli Bidiyo: An kama Dan Banga, da suka je kama me Gàrkùwà da mutane suka iske baya nan sai suka yiwa matarsa Fyàdè

Kalli Bidiyo: An kama Dan Banga, da suka je kama me Gàrkùwà da mutane suka iske baya nan sai suka yiwa matarsa Fyàdè

Duk Labarai
Wani dan banga da aka kama ya dauki hankula a kafafen sada zumunta saboda laifin da ya aikata. Sun je kama me garkuwa da mutanene sai suka tarar da baya gida amma sai matarsa https://twitter.com/Dongarrus1/status/1932060506275061812?t=hIo8JSRAwGBbjGq1El7PyQ&s=19 Anan suka nemi yin lalata da ita kuma ta basu hadin kai, saidai daga baya an kamasu.
Tinubu ne ke daukar nauyin rikicin dake faruwa a jam’iyyar mu ta Labour party>>Peter Obi

Tinubu ne ke daukar nauyin rikicin dake faruwa a jam’iyyar mu ta Labour party>>Peter Obi

Duk Labarai
Dan takarar shugaban kasa na jam'iyyar Labour party, Peter Obi ya bayyana cewa, shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ne ke da alhakin rikicin dake faruwa a cikin jam'iyyar su. Obi ya bayyana hakane a yayin da ake masa tambayoyi a gidan Talabijin na Arise TV inda yace yana da tabbacin Gwamnatin tarayya ce ta dauki nauyin rikicin dake faruwa a jam'iyyar. Ya bayyana cewa, suna son yada rikici a cikin jam'iyyar ta Labour Party.
Jigo a Jam’iyyar PDP, Segun Sowunmi yace a shirye yake ya koma APC duk da a baya ya soki jam’iyyar

Jigo a Jam’iyyar PDP, Segun Sowunmi yace a shirye yake ya koma APC duk da a baya ya soki jam’iyyar

Duk Labarai
Jigo a jam'iyyar PDP, Segun Sowunmi ya bayyana cewa, a Shirye yake ya koma jam'iyyar APC duk da a baya ya soki jam'iyyar da salon mulkin shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu. Ya bayyana hakane a wata hira da aka yi dashi a gidan talabijin na Channels TV. Yace lallai a baya ya soki Gwamnatin Tinubu amma a yanzu idan dai ya samu dama, zai iya komawa jam'iyyar APC. Yace kuma a shirye yake dan yin aiki tare da shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu din domin ko da a baya dama yayi aiki tare dashi.