Monday, December 15
Shadow
Da Duminsa: Dangantaka tsakanin Amurka da Israyla na kara tsami, yanzu haka mataimakin shugaban kasar Amurka, JD. Vance ya soke ziyarar da yake shirin kaiwa kasar saboda rashin jin dadin fadada hàrè-hàrèn da Israyla ke kaiwa Gàzà

Da Duminsa: Dangantaka tsakanin Amurka da Israyla na kara tsami, yanzu haka mataimakin shugaban kasar Amurka, JD. Vance ya soke ziyarar da yake shirin kaiwa kasar saboda rashin jin dadin fadada hàrè-hàrèn da Israyla ke kaiwa Gàzà

Duk Labarai
Rahotannin dake fitowa daga kasar Amurka na cewa, Mataimakin shugaban kasar, JD. Vance ya fasa kai ziyarar da yayi niyya zuwa kasar Israela. An bayyana cewa rashin jin dadin fadada hare-haren Israyla a Gaza ne yasa JD. Vance daukar wannan mataki. Dama dai a baya hutudole.com ya kawo muku rahoton cewa, Amurka na shirin amincewa da kafuwar kasar Palasdinu saboda an samu rashin jituwa tsakanin kasashen Biyu. Trump dai bai san ana juyashi yayin da rahotanni ke cewa, shi kuma shugaban Israela Benjamin Netanyahu yana son ya rika juya shuwagabannin Amurka.
Da Duminsa: Peter Obi yayi magana me dadi game da Rahoton dake cewa ya yadda ya zama mataimakin Atiku a 2027

Da Duminsa: Peter Obi yayi magana me dadi game da Rahoton dake cewa ya yadda ya zama mataimakin Atiku a 2027

Duk Labarai
A yayin rahoto yayi nisa cewa dan takarar shugaban kasa a karkashin jam'iyyar Labour party a shekarar 2023, Peter Obi ya yadda yawa Atiku Abubakar mataimakin shugaban kasa a zaben shekarar 2027, Peter Obi din yayi martani kan wannan rahoton. Peter obi dai bai karyata wannan rahoto ba amma yace Koma me za'a fada aje ai ta fada amma shi yayi hadaka dan kawar da matsalar rashin tsaro da yunwa a Najeriya. Ya bayyana hakane a Kubawa Abuja wajan wani taro inda ya bayar da tallafi ga wata Makaranta. Dama dai a shekarar 2019, Peter Obi da Atiku ne suka tsaya takarar shugabancin Najeriya amma tsohon shugaban kasa, Muhammadu Buhari ya kadasu.
Ji Yadda Gwamna Abba Gida-gida ya taimaki dalibar da ke fama da lalura bayan ta tura masa sako na neman taimako

Ji Yadda Gwamna Abba Gida-gida ya taimaki dalibar da ke fama da lalura bayan ta tura masa sako na neman taimako

Duk Labarai
Yadda Gwamna Abba Gida-gida ya taimaki dalibar da ke fama da lalura bayan ta tura masa sako na neman taimako. A cikin wani lamari mai ratsa zuciya , wata mata mai karfin gwiwa da buri, Mai suna Ummi mai shekaru 31, ta samu kulawar da ta daɗe tana mafarki daga gwamnatin Kano karkashin jagorancin Gwamna Alhaji Abba Kabir Yusuf. Ummi ta shafe kusan shekaru 18 tana fama da wata cuta mai suna Proximal Myopathy, wadda ke sa raunin tsokokin jiki. Duk da wannan ƙalubale, ta kammala karatunta a fannin shari'a, amma rashin lafiya ya hana ta zuwa makarantar koyon aikin lauya (Law School). Duk da rashin tabbacin amsa, Ummi ta aike da saƙon neman agaji ga Gwamna Abba Kabir Yusuf. Cikin abin mamaki da tausayawa, Gwamna ya karanta saƙon kuma ya ɗauki matakin gaggawa. Wani faifan bidiyo da ya...
NNPP ta nemi afuwar Tinubu kan kalaman suka da ake zargin Kwankwaso ya yi masa

NNPP ta nemi afuwar Tinubu kan kalaman suka da ake zargin Kwankwaso ya yi masa

Duk Labarai
Jam’iyyar NNPP ta nemi afuwar Shugaban kasa Bola Tinubu da kuma jam’iyya mai mulki ta APC dangane da wasu kalaman suka da dan takararta na shugaban kasa a zaben 2023, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, ya yi a kwanakin baya. Jam’iyyar ta gargadi Kwankwaso da kada ya kara amfani da sunanta wajen sukar Shugaba Tinubu da jam’iyyar APC, tana mai cewa tsohon gwamnan jihar Kano an kore shi daga NNPP tuni. A wata sanarwa da sakataren yada labarai na kasa na NNPP, Dakta Oginni Olaposi, ya fitar a ranar Lahadi a Legas, jam’iyyar ta nesanta kanta daga kalaman Kwankwaso, inda ta bayyana cewa an katse duk wata alaka tsakaninta da Kwankwaso da kuma kungiyar Kwankwasiyya da yake jagoranta. “Muna neman afuwa ga Shugaban kasa Bola Tinubu da dukan iyalan jam’iyyar APC, karkashin jagorancin Dakta Abdulla...
Kalli Bidiyon yanda aka hana Peter Obi shiga wajan da manyan mutane ke zaune a wajan rantsar da Fafaroma

Kalli Bidiyon yanda aka hana Peter Obi shiga wajan da manyan mutane ke zaune a wajan rantsar da Fafaroma

Duk Labarai
A yayin da bodiyon dan shugaban kasa, Seyi Tinubu ke ta yawo inda aka ganshi an hanashi gaisawa da Fafaroma Leo XIV a Vatican. A yanzu kuma Bidiyon Peter Obi ne ya bayyana inda aka ganshi shi kuma an hanashi shiga wajan da aka tanadarwa manyan mutane. Lamarin ya dauki hankula a kafafen sada zumunta. https://twitter.com/SaharaReporters/status/1924501545959166428?t=01bdLGGmnrdP3fksH7fk_Q&s=19 Mutane da yawa sun bayyana ra'ayoyi akai.
Nan ba Najeriya ba ce”: Jami’ian tsaron fadar Vatican sub hana Seyi shiga wajen taron Tinubu da Fafaroma

Nan ba Najeriya ba ce”: Jami’ian tsaron fadar Vatican sub hana Seyi shiga wajen taron Tinubu da Fafaroma

Duk Labarai
“Nan ba Najeriya ba ce”: Jami'ian tsaron fadar Vatican sub hana Seyi shiga wajen taron Tinubu da Fafaroma. Seyi Tinubu, ɗan Shugaba Bola Tinubu, ya kasance cikin jerin waɗanda su ka raka shi zuwa bikin rantsar da Fafaroma Leo XIV a ranar Lahadi. Jaridar Daily Trust ta rawaito muhimman abubuwan da suka faru a wajen bikin, ciki har da ganawar da shugaba Tinubu ya yi da Peter Obi, ɗaya daga cikin manyan abokan hamayyarsa a zaɓen 2023. https://twitter.com/harreceipts/status/1924155639275659456?t=qnZ8k_3TtTZ2l29ng8GJbQ&s=19 Obi, wanda ya zo na uku a zaɓen, ya doke Tinubu a jihar Legas — inda Shugaba Tinubu ke da rinjaye tun dawowar dimokuraɗiyya a Najeriya a 1999. Daya daga cikin abubuwan da suka jawo hankali a tafiyar zuwa birnin Vatican ita ce mu'amalar da ɗan Shugaba...
Kuma Dai:An kara kama wasu masu Gàrkùwà da mutane su 4 dake kan hanyar zuwa Makkah aikin Hajji

Kuma Dai:An kara kama wasu masu Gàrkùwà da mutane su 4 dake kan hanyar zuwa Makkah aikin Hajji

Duk Labarai
Rahotannin da hutudole ke samu na cewa bayan Yahaya Zango wanda aka kama jiya a Abuja wanda rikakken dan Bindiga ne da jami'an tsaro suka dade suna nema tare da Alhazai masu shirin zuwa Makkah Aikin Hajji, An sake kama wasu mutane 4 suma a Abujan. Mutanen da aka kama sun hada da wata mata da ake zargin Mahaifiyace ga dan Bindiga Gwaska Dankarami, da kuma Madele wanda shi kuma mahaifin dan Bindiga Ado Aliero ne sai kuma wani me suna Bello Bazamfare. Rahoton yace wani kuma da aka kama tare dasu ana zargin dan uwan Ado Aliero. A shekarar data gabata ma dai an samu rahotannin 'yan Bindiga 14 da suka je aikin Hajji.
An kwashe maniyyatan jihohin Najeriya 12 – NAHCON

An kwashe maniyyatan jihohin Najeriya 12 – NAHCON

Duk Labarai
Ma'aikaar kula da aikin hajji ta Najeriya ta bayyana cewa an kwashe maniyyata aikin hajji daga jahohi 12 na ƙasar, waɗanda yawansu ya kai mutum 25,702. Jihohin su ne Osun da Oyo da Adamawa da Filato da Ekiti Imo da Legas da Abiya kuma Edo. Hukumar alhazan ta ce an kwashe wannan adadin ne bayan sawu 63 daga Najeriya zuwa Saudiyya a cikin kwana goma. Kawo yanzu dai hukumar ta ce babu wata matsala da aka fuskanta tun bayan soma jigilar maniyyatan, inda a wannan shekarar hukumomin suka ce mutum 43,000 ne za su sauke farali a ƙasar ta Saudiyya domin gudanar da babbar ibadar ta Musulmai. A ckin wata sanarwa da jami'in gudanarwar hukumar na ƙasa, Ibrahim Muhammad ya sanya wa hannu, ya bayyana cewa matakan da hukumar ta ɗauka da ke kan tsari sun taimaka matuƙa inda jigilar maniyyatan d...
‘Yan Bìndìgà sun yi gàrkuwà da babban Basarake a Arewacin Najeriya

‘Yan Bìndìgà sun yi gàrkuwà da babban Basarake a Arewacin Najeriya

Duk Labarai
Wasu ƴanbidga sun kai hari garin Okoloke da ke ƙaramar hukumar Yagba ta yamma a jihar ta Kogi, inda suka kashe aƙalla mutum uku are da jikkata wasu da dama. Maharan sun kuma yi garkuwa da babban basaraken al'ummar ta Okoloke, Pa Dada James Ogunyanda, a lokacin da ake tsaka da zaman fadanci, wanda bayanai suka tabbatar da cewa ba shi da cikakkiyar lafiya kuma yana daf da tafiya neman magani, kamar yadda gidan talbijin na Channels ya ruwaito. 'Yan bindigar sun kuma kashe ƴanbanga biyu da wani ma'aikacin kamfanin sadarwa da ke aikin gyaran ƙarfen samar da sabis a yankin. Rahotanni sun ce 'yan bangar na samar wa ma'aikacin sadarwar tsaro ne lokacin da maharan suka yi musu kwanton ɓauna inda suka buɗe musu wuta nan take. Hare-haren 'yan bindiga dai na ci aba da ƙaruwa a baya-bayan n...
Talauci ne tushen matsalar tsaron arewacin Najeriya – Gwamnan Kaduna

Talauci ne tushen matsalar tsaron arewacin Najeriya – Gwamnan Kaduna

Duk Labarai
Gwamnan jihar Kaduna Uba Sani ya ce tsansar talauci da koma bayan tattalin arziki su ne manyan abubuwan da ke haifar da masaloli tsaro a yankin arewacin Najeriya, inda ya yi gargaɗin cewa muddin ba a magance su gaba ɗaya ba to yankin zai ci gaba da fuskantar matsalolin tashe-tashen hankaln. Gwamnan ya bayyana hakan a cikin shirin siyasa na Sunday Politics na gidan talibijin na Channels, inda ya ce gwamnatinsa ta soma ne da fito da hanyoyin yaƙi da talauci da rashin aikin yi tsakanin matasa, inda ya alaƙanta hakan ga irin ƙwarewar da ya ya samu lokacin da ya ke shugaban kwamitin da ke lura da bankuna na majalisar dattawan a lokacin yana ɗan majalsar dattawan. "Lokacin da aka zaɓe ni a matsayin gwamnan Kaduna, abinda na soma yi shi ne duba girman matsalar talaucin da ake fama...