Friday, December 5
Shadow
Nice wadda aka fi tattauna batunta a kafafen sada zumunta a Arewa, dan haka duk wanda yasa ya taba yin magana akai na amma bai yi magana akan daliban jihar Kebbi ba, Na Zhaghi Babansa>>Inji Tauraruwar fina-finan Hausa, Fatima Hussain

Nice wadda aka fi tattauna batunta a kafafen sada zumunta a Arewa, dan haka duk wanda yasa ya taba yin magana akai na amma bai yi magana akan daliban jihar Kebbi ba, Na Zhaghi Babansa>>Inji Tauraruwar fina-finan Hausa, Fatima Hussain

Duk Labarai
Tauraruwar fina-finan Hausa, Fatima Hussain ta bayyana cewa, duk wanda itace aka fi tattauna batunta a kafafen sada zumunta na Arewa. Tace dan haka duk wanda yasan ya taba magana a kanta, a yanzu tana son ya fito yayi magana akan dalibai mata na jihar Kebbi da aka yo garkuwa dasu. Tace duk wanda bai yi ba ta zagi Ubansa. https://www.tiktok.com/@fateeemahussain/video/7574392226738998549?_t=ZS-91WwhOqWW2K&_r=1
A karshe dai: Fitsararriyar mawakiyar Amurka, Nicki Minaj ta je Majalisar Dinkin Duniya inda tace Ana Mhuzghunawa Kiristoci a Najeriya kuma ya kamata a Ki Khari a cece su

A karshe dai: Fitsararriyar mawakiyar Amurka, Nicki Minaj ta je Majalisar Dinkin Duniya inda tace Ana Mhuzghunawa Kiristoci a Najeriya kuma ya kamata a Ki Khari a cece su

Duk Labarai
Fitsararriyar mawakiyar Amurka, Nicki Minaj ta je majalisar Dinkin Duniya inda ta bayyana cewa ana yiwa Kiristoci Khisan Kyiyashi a Najeriya. Ta bayyana cewa ya kamata a kawo musu dauki dan hakan taimakon al'umma ne baki daya. Ta kuma yi kiran a dauki mataki ama dukkan sauran kasashen Duniya da irin wannan abu ke faruwa
Tabbas Najeriya na bukatar dauki ka gaggauta zuwa ka ceci kasarnan>>Sabon Shugaban PDP, Tanimu Turaki ya roki Shugaban kasar Amirka, Donald Trump

Tabbas Najeriya na bukatar dauki ka gaggauta zuwa ka ceci kasarnan>>Sabon Shugaban PDP, Tanimu Turaki ya roki Shugaban kasar Amirka, Donald Trump

Duk Labarai
Sabon Shugaban jam'iyyar PDP, Tanimu Turaki ya roki shugaban kasar Amurka, Donald Trump da ya gaggauta kawo sauki Najeriya dan ya ceci kasar. Ya bayyana hakane bayan samun shiga cikin hedikwatar jam'iyyar PDP bayan da jami'an tsaro suka hanashi shiga da farko. Tanimu Turaki yace Trump ya zo ya ceci Dimokradiyyar Najeriya daga hannun wadanda ke son lalatata. Yace Ba Mhuzghunawa Kiristoci kadai ake yi a Najeriya ba hadda ma wulakanta Dimokradiyya. Saidai fadar shugaban kasa ta bakin me magana da yawun shugaban kasa, Bayo Onanuga ya bayyana cewa wadannan kalaman na Tanimu Turaki cin amanar kasa ne kuma ba za'a manta dasu ba.
Tinubu zai je Afirka ta Kudu da Angola

Tinubu zai je Afirka ta Kudu da Angola

Duk Labarai
Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu zai bar ƙasar a yau Laraba domin halartar taron G20 da taro tsakanin kungiyar Tarayyar Turai da ta Tarayyar Afirka. ‎Shugaban zai soma ziyarar ne a Johannesburg,babban birnin ƙasar Afrika ta kudu, inda zai halarci karo na ashirin na taron shugabannin ƙasashe ashirin masu ƙarfin tattalin arziƙi wato G20 a ranakun 22 da 23 ga watan Nuwamba. Daga nan zai tafi birnin Luanda da ke Angola domin halartar taron kungiyar Tarayyar Turai da Tarayyar Afirka karo na 7 a ranakun 24 da 25 ga watan Nuwamban 2025. Waɗannan bayanai na ƙunshe ne a cikin sanarwa da mai magana da yawun shugaban Bayo Onanuga ya fitar a babban birnin ƙasar Abuja, kamar yadda kamfanin dillancin labarai na Najeriya ya ruwaito. Ana kuma sa ran Shugaba Tinubu zai yi wasu gana...
Tinubu ya jajanta wa iyalan Birgediya Janar Musa Uba

Tinubu ya jajanta wa iyalan Birgediya Janar Musa Uba

Duk Labarai
Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya tabbatar da mutuwar jami'in sojan ƙasar Birgediya Janar Musa Uba, wanda mayaƙan ƙungiyar Iswap suka kashe a jihar Borno. An fara fargabar mutuwar Janar Uba ne bayan ƙungiyar ta yi iƙirarin kashe shi, da kuma fitar da wani bidiyo. Wata sanarwa da rundunar sojan Najeriya ta fitar ta ce a ƙarshen makon da ya gabata ne 'yanbindigar suka yi wa dakarunta kwanton ɓauna, waɗanda janar ɗin ke jagoranta. Zuwa yanzu rundunar ba ta ce komai ba game da bidiyon da ke yawo a intanet. Sai dai cikin wata sanarwa da mai magana da yawun shugaban ƙasa, Bayo Onanuga, ya fitar ranar Talata, Shugaba Tinubu ya ce mutuwar janar ɗin "ta kaɗa" shi. "A matsayina na babban kwamandan tsaro na ƙasa, na ji takaici da mutuwar sojojinmu a bakin aiki. Allah ya bai wa iyalan Bi...
Wata Kungiyar ‘yan Najeriya mazauna kasashen waje tace Shugaba Trump ya gaggauta kawo Khari Najeriya inda tace Ana kokarin mayar da kasar Kasar Musulinci ce

Wata Kungiyar ‘yan Najeriya mazauna kasashen waje tace Shugaba Trump ya gaggauta kawo Khari Najeriya inda tace Ana kokarin mayar da kasar Kasar Musulinci ce

Duk Labarai
Wata kungiya me suna The Global Coalition for Security and Democracy in Nigeria ta 'yan Najeriya wadda suka kafa a kasar Amirka tace ta yi na'am da Amurka ta saka Najeriya cikin kasashen da zata rika sakawa ido. Kumgiyar tace tana kira ga shugaban kasar Amurka, Donald Trump da ya gaggauta kawo Kharin da yace zai kawo Najeriya. Kungiyar ta bayyana hakane a sanarwar data fitar ta bakin shugabanta, Comrade Frederick Odorige inda tace tana goyon karfafa tsaro da Dimokradiyya a Najeriya.
Kaso 90 na Musulman Najeriya Sunni ne, Inji Tsohon Hadimin Shugaban kasa, Malam Bashir Ahmad

Kaso 90 na Musulman Najeriya Sunni ne, Inji Tsohon Hadimin Shugaban kasa, Malam Bashir Ahmad

Duk Labarai
Tsohon Hadimin Shugaban kasa, Malam Bashir Ahmad ya bayyana cewa, kaso 90 na musulman Najeriya Sunni ne. Ya bayyana hakane a martanin da yakewa 'Yar siyasar kasar Canada, Goldie Ghamari inda tace Najeriya na hada kai da kasar Iran dan Khasye Kiristoci. Yace abinda ma bata sani ba shine kaso 90 na musulman Najeriya Sunni ne. Yace 'yan kasar waje suna amfani da rarrabuwar mu ne wajan cimma burinsu inda yace sai mun hada kai. https://twitter.com/BashirAhmaad/status/1990889063834861572?t=RKCwoiSicU5RhxOM7Q_0VA&s=19
Allah Sarki Kalli Bidiyon: Yanda Tauraruwar Kannywood, Fatima Hussain Cikin kuka tare Alhinin abinda akawa daliban makarantar mata ta jihar Kebbi

Allah Sarki Kalli Bidiyon: Yanda Tauraruwar Kannywood, Fatima Hussain Cikin kuka tare Alhinin abinda akawa daliban makarantar mata ta jihar Kebbi

Duk Labarai
Tauraruwar fina-finan Hausa, Fatima Hussain ta fito ta bayyana takaici kan garkuwa da dalibai mata 25 da aka yi a jihar Kebbi. Ta bayyana hakane a shafinta na sada zumunta inda tace idan ba'a so a yi karatu ne a kulle makarantun mana. Tace duka yaushe aka sace dalibai mata amma gashi an sake yi. Tace daliban na da kananan shekaru. https://www.tiktok.com/@fateeemahussain/video/7574376952191028500?_t=ZS-91WmE2naJV3&_r=1
Innalillahi wa’inna ilaihi raji’un Kalli Bidiyon Da Duminsa: Mummunan Abinda Tshagyeran dhajiy sukawa Sojowjin da aka aika su kubutar da dalibai ‘yan mata ‘yan makarantar jihar Kebbi

Innalillahi wa’inna ilaihi raji’un Kalli Bidiyon Da Duminsa: Mummunan Abinda Tshagyeran dhajiy sukawa Sojowjin da aka aika su kubutar da dalibai ‘yan mata ‘yan makarantar jihar Kebbi

Duk Labarai
Rahotanni da Duminsa sun bayyana cewa 'yan Bìndìgà a Daji sun afkawa sojojin da aka aika su kubutar da dalibai 'yan mata da aka yi garkuwa dasu a jihar Kebbi. A Bidiyon wanda kafar Sahara Reporters ta wallafa, an ga sojojin kwakkwance cikin Jiyni wasu an Harbesu a kafa wasu a sassa daban-daban na jikinsu. Dalibai mata 25 ne dai 'yan Bìndìgàr suka yi garkuwa dasu inda wasu biyu suka kubuta. Danna nan dan kallon Bidiyon https://twitter.com/SaharaReporters/status/1991074295015997845?t=50Y5DUr-jQN8s0-V8zdaXQ&s=19