Monday, December 15
Shadow
Talauci ne tushen matsalar tsaron arewacin Najeriya – Gwamnan Kaduna

Talauci ne tushen matsalar tsaron arewacin Najeriya – Gwamnan Kaduna

Duk Labarai
Gwamnan jihar Kaduna Uba Sani ya ce tsansar talauci da koma bayan tattalin arziki su ne manyan abubuwan da ke haifar da masaloli tsaro a yankin arewacin Najeriya, inda ya yi gargaɗin cewa muddin ba a magance su gaba ɗaya ba to yankin zai ci gaba da fuskantar matsalolin tashe-tashen hankaln. Gwamnan ya bayyana hakan a cikin shirin siyasa na Sunday Politics na gidan talibijin na Channels, inda ya ce gwamnatinsa ta soma ne da fito da hanyoyin yaƙi da talauci da rashin aikin yi tsakanin matasa, inda ya alaƙanta hakan ga irin ƙwarewar da ya ya samu lokacin da ya ke shugaban kwamitin da ke lura da bankuna na majalisar dattawan a lokacin yana ɗan majalsar dattawan. "Lokacin da aka zaɓe ni a matsayin gwamnan Kaduna, abinda na soma yi shi ne duba girman matsalar talaucin da ake fama...
Karanta Jadawalin jami’o’in Najeriya dake bada Admission da makin Jamb 140, 150, da 160

Karanta Jadawalin jami’o’in Najeriya dake bada Admission da makin Jamb 140, 150, da 160

Duk Labarai
Yayin da aka kammala jarabawar JAMB ta shiga jami'a, Mun kawo muku jadawalin jami'o'in dake amincewa da makin JAMB 140,150, da 160 wajan bayar da Admission. Jadawalin jami'o'in dake bayar da Admission da maki 160 a Najeriya: 1. Abia State University 2. Achievers University 3. Akwa Ibom State University 4. Al-Qalam University 5. American University of Nigeria 6. Augustine University 7. Babcock University 8. Bowen University 9. Covenant University 10. Edo University 11. Igbinedion University 12. Joseph Ayo Babalola University 13. Madonna University 14. Nile University of Nigeria 15. Oduduwa University 16. Pan-Atlantic University 17. Paul University 18. Redeemer’s University 19. Renaissance University 20. Rhema University 21. ...
Wata Sabuwa: Bankin Fidelity na fuskantar Talaucewa

Wata Sabuwa: Bankin Fidelity na fuskantar Talaucewa

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa, Bankin Fidelity Bank na fuskantar barazanar durkushewa. Hakan ya bayyana ce bayan da Kotun Koli ta bukaci bankin ya biya wani bashi na Naira Biliyan N225 da ake binsa. Bankin dai idan har zai biya wadannan kudade rahoton yace durkushewa zai yi. Saidai wasu masana harkar bankin sun ce basa tunanin babban bankin Najeriya, CBN ,zai bari bankin ya durkushe, zai iya kai masa dauki.
Peter Obi ya amince ya zama mataimakin Atiku a takarar 2027 da sharadin cewa idan sun ci zabe Atiku zango daya zai yi ya sauka

Peter Obi ya amince ya zama mataimakin Atiku a takarar 2027 da sharadin cewa idan sun ci zabe Atiku zango daya zai yi ya sauka

Duk Labarai
Rahotanni da hutudole ke samu na cewa, Peter Obi wanda dan takarar shugaban kasa ne a shekarar 2023 ya mince ya zama mataimakin Atiku Abubakar a zaben 2027. Rahotan wanda kafar jaridar Punchng ta ruwaito yace an yi zaman tattaunawa tsakanin Atiku da Peter Obi a kasar Ingila wanda a canne aka cimma wannan matsaya. Da farko dai Atiku ya gayawa Peter Obi cewa ya zama mataimakinsa shi kuma zai yi zango data ne kawai ya sauka, Peter Obi yace a bashi lokaci zai je yayi Shawara. Saidai Rahotan yace Tuni Peter Obi ya amince da wannan tayi. A shekarar 2019 dai Peter Obi da Atiku sun yi takara tare amma tsohon shugaban kasa, Muhammadu Buhari ya kayar dasu.
Wallahi Hulata tafi Madugun Iska, Jahili(Kwankwaso), Kuma na fishi iya Turanci>>Alhassan Ado Doguwa

Wallahi Hulata tafi Madugun Iska, Jahili(Kwankwaso), Kuma na fishi iya Turanci>>Alhassan Ado Doguwa

Duk Labarai
{"remix_data":[],"remix_entry_point":"challenges","source_tags":[],"origin":"unknown","total_draw_time":0,"total_draw_actions":0,"layers_used":0,"brushes_used":0,"photos_added":0,"total_editor_actions":{},"tools_used":{},"is_sticker":false,"edited_since_last_sticker_save":false,"containsFTESticker":false} Dan majalisar Wakilai daga jihar Kano, Alhassan Ado Doguwa ya bayyana cewa yafi Tsohon Gwamnan jihar, Dr. Rabiu Musa Kwankwaso iya Turanci. Sannan ya ce hularsa ta fi Kwankwaso, ya bayyana hakane a wajan wani jawabi da yayi a gaban al'ummar mazabarsa da ya yadu sosai a kafafen sada zumunta. Kalli Bidiyon a kasa: https://twitter.com/tudunwada__mi/status/1924098827432149440?t=vBKrLSgx2T5RSFf6J5VdWQ&s=19 Ga dayan Bidiyon: https://twitter.com/tudunwada__mi/status/1924...
Binani ta ƙara sayo sabon jirgi domin fara jigilar fasinja

Binani ta ƙara sayo sabon jirgi domin fara jigilar fasinja

Duk Labarai
{"remix_data":[],"remix_entry_point":"challenges","source_tags":[],"origin":"unknown","total_draw_time":0,"total_draw_actions":0,"layers_used":0,"brushes_used":0,"photos_added":0,"total_editor_actions":{},"tools_used":{},"is_sticker":false,"edited_since_last_sticker_save":false,"containsFTESticker":false} Kamfanin Sufurin Binani Air mallakin tsohuwar ƴan takarar gwamnan jihar Adamawa a zaɓen 2023 Sanata Aishatu Ɗahiru Binani ya ƙara sayo sabon jirgi a shirye-shiryen shi na fara aikin jigilar fasinja a Najeriya. Binani Air wanda ya samu lasisin fara wannan aikin lokacin ɗaya da kamfanin sufurin Rano Air, Hausa Daily Times ta gano kamfanin ya samu jinkirin fara wannan aikin a sakamakon wasu dalilai da ba kowa ya sani ba amma dai ana ganin bai rasa nasaba da rashin ƙarasowsn sauran jira...
“Wallahi yanzu haka in da zan bayar da duk abin da na mallaka don in koma gida zan yi hakan, idan na koma gida sai na zuba ruwa a ƙasa na sha, na yi sujada don gode wa Ubangiji.” Inji Matashin Najeriya dake shan Wahala A Kasar Libya

“Wallahi yanzu haka in da zan bayar da duk abin da na mallaka don in koma gida zan yi hakan, idan na koma gida sai na zuba ruwa a ƙasa na sha, na yi sujada don gode wa Ubangiji.” Inji Matashin Najeriya dake shan Wahala A Kasar Libya

Duk Labarai
"Wallahi yanzu haka in da zan bayar da duk abin da na mallaka don in koma gida zan yi hakan, idan na koma gida sai na zuba ruwa a ƙasa na sha, na yi sujada don gode wa Ubangiji." Wannan ne kalami na ƙarshe da Mukhtar ya faɗa min a tattaunawar da na yi da shi game da tafiyarsa da kuma zaman da yake yi yanzu haka a Libya. Yana daga cikin dubban matasan da ke ficewa daga ƙasashen Yammacin Afirka domin zuwa neman rayuwa mai kyau a ƙasashen Turai ta ɓarauniyar hanya, waɗanda akasarinsu kan faɗa tarkon ƙungiyoyin masu riƙe da makamai a ƙasashen yankin arewacin Afirka. Da dama daga cikinsu kan gamu da ajalinsu, ko dai a kan hanyarsu ta tafiya ko kuma a lokacin da suka tsinci kansu a ƙasashe irin Libya inda ƙungiyoyin ƴanbindiga ke yaƙi da juna sanadiyyar raunin hukumomi. Su kuma waɗan...
Shugaba Tinubu ya amince da bayar da lasisin fara aikin hakar mai a Kolmani dake tsakanin Bauchi da Gombe

Shugaba Tinubu ya amince da bayar da lasisin fara aikin hakar mai a Kolmani dake tsakanin Bauchi da Gombe

Duk Labarai
LABARI MAI ZAFI: Shugaba Bola Tinubu ya bayar da amincewar doka don fitar da dukkan muhimman lasisi da ake bukata domin aiwatar da aikin Kolmani Integrated Development Project, wani katafaren shirin hakar man fetur da darajarsa ta kai biliyoyin daloli, wanda yake tsakanin jihohin Bauchi da Gombe. Idan har ta kasance za muyi farin ciki da hakan .Alllah yasa kuma ba shirin zaben 2027 ba ne
Gobara ta tashi a makarantar Qur’ani ta Sheikh Dahiru Bauchi dake Rafin Albasa, Bauchi

Gobara ta tashi a makarantar Qur’ani ta Sheikh Dahiru Bauchi dake Rafin Albasa, Bauchi

Duk Labarai
Rahotanni daga jihar Bauchi na cewa, Gobara ta tashi a makarantar Sheikh Dahiru Usman Bauchi dake Rafin Albasa a jihar. Rahoton Daily Trust yace Gobarar ta cinye ginin wanda benene inda ta lalata kayan aiki dake ofis-ofis na cikin ginin. Zuwa yanzu dai ba'a gano dalilin faruwar Gobarar ba. Shugaban Gidauniyar Dahiru Bauchi, Sayyadi Aliyu Sise Dahiru ya jajantawa dalibai da malaman makarantar kan wannan ibtila'i. Yace sun godewa Allah da ba'a samu asarar rai ba. Yace Sheikh Dahiru Bauchi ne ya kafa makarantar inda Tsohon mataimakin shugaban kasa, Namadi Sambo ya budeta. Yacw an yi asarar litattafai na malam da na marigayi Sheikh Hadi Dahiru Bauchi, dana Ahmad Sheikh Dahiru da sauransu. Yace gobarar ta tashine bayan an tashi daga makarantar.