Thursday, March 12
Shadow
Tinubu Rahama ne ga Najeriya, Ya hana mutane da yawa mutuwa>>Inji Kungiyar kare muradin Yarbawa ta YCG

Tinubu Rahama ne ga Najeriya, Ya hana mutane da yawa mutuwa>>Inji Kungiyar kare muradin Yarbawa ta YCG

Duk Labarai
Kungiyar kare muradun yarbawa ta YCG ta bayyana shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu a matsayin shugaba na gari wanda rahama ne ga 'yan Najeriya. Kungiyar tace tsare-tsaren shugaba Tinubu sun taimaka wajan samar da tsaro, ga rayuwa da dukiyoyin jama'a. Kungiyar tace a cikin shekaru 2 da shugaba Tinubu yayi yana mulki, Gwamnatinsa ta samar da tsaro da kara karfin tattalin arzikin Najeriya. Wakilan Kungiyar Olugbemga Oyewusi, Mrs Buky Tunde Oshunrinde, ne suka bayyana hakan a sanarwar da suka fitar ga manema labarai. Sun ce Yabo Shugaba Tinubu ya cancanta ba barazana da zagi ba.
Gwamnan Kano ya jagoranci tawogar Kano da Jigawa zuwa halartar jana’izar Dantata a Madina

Gwamnan Kano ya jagoranci tawogar Kano da Jigawa zuwa halartar jana’izar Dantata a Madina

Duk Labarai
Gwamnan Kano ya jagoranci tawogar Kano da Jigawa zuwa halartar jana'izar Dantata a Madina. Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya tashi daga Filin Jirgin Sama na Malam Aminu Kano, inda yake jagorantar wata babbar tawaga domin halartar jana’izar fitaccen attajiri kuma dattijon kasa, marigayi Alhaji Aminu Alhassan Dantata, a birnin Madina mai alfarma, da ke Kasar Saudiyya. Marigayin ya rasu da safiyar Asabar a birnin Abu Dhabi na Hadaddiyar Daular Larabawa. Wannan bayanin na cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sanusi Bature Dawakin Tofa, ya fitar. Tawagar tana dauke da Sarkin Kano, Khalifa Muhammadu Sanusi II, Gwamnan Jihar Jigawa, Alhaji Umar Namadi, tsohon gwamnan Jigawa Barr. Ali Sa’ad Birnin Kudu, da wasu manyan jami’an gwamnati da fitattun dattawa...
Kamfanonin Dangote sun zo na daya a Afrika wajan samar da kayan Masarufi a shekarar 2025

Kamfanonin Dangote sun zo na daya a Afrika wajan samar da kayan Masarufi a shekarar 2025

Duk Labarai
Kamfanonin Dangote ne suka zo na daya a Nahiyar Africa wajan samar da kayan Masarufi na yau da kullun a shekarar 2025. Kafar The African Exponent ce wadda ta shahara wajan samar da bayanan kasuwanci ta bayyana hakan. Face Dangote ya zo na daya da kamfanoninsa na Sugar, Gishiri, Taliya da Macaroni da sauransu. Kamfanin Nestlé dake yin Milo, Nescafé, Cerelac, da Maggi ne ya zo na biyu inda yake da rassa a kasashen Nigeria, Ghana, South Africa, da Côte d’Ivoire. Daga nan kuma sai kamfanin Unilever wanda ya zo na 3, shine ke yin OMO, Close-Up, Lipton, Vaseline, da magin Knorr. Kuma yana da rassa a kasashe kusa 20 na Afrika. Kamfanin Africa ta kudu me sunan Tiger Brands ne ya zo na 4. Sai kamfanin SABMiller AB InBev wanda shima na kasar Africa ta kudi ne ya zo na 5. Kamf...
Babu tsageran da ya fi karfin mu a kasarnan>>Inji Janar din Soja

Babu tsageran da ya fi karfin mu a kasarnan>>Inji Janar din Soja

Duk Labarai
Major General Ijioma Nwokoro Ijioma ya bayyana cewa, babu dan ta'addar da ya fi karfin sojojin Najeriya. Janar din me ritaya na daga cikin wadanda aka tura zuwa kasar Sudan dan kwantar da tarzoma a tsakanin shekarun 2013 zuwa 2015. Hakanan ya yaki kungiyar Bòkò Hàràm inda ya kwato karamar hukumar dake hannunsu. Janardin wanda akawa ritayar dole ya bayyana cewa matsalar Najeriya shugabanci ne kuma shiyasa shuwagabannin saboda sun san basu da nagarta sai su rika amfani da kabilanci da addini wajan neman nasarr cin zabe.
Ji sunayen Gwamnoni 5 da zasu koma APC saboda goyon bayan sake zaben shugaba Tinubu a 2027

Ji sunayen Gwamnoni 5 da zasu koma APC saboda goyon bayan sake zaben shugaba Tinubu a 2027

Duk Labarai
Jam'iyyar APC tace akwai karin Gwamnoni 5 da zasu koma jam'iyyar nan da watanni 2. Mataimakin shugaban jam'iyyar daga yankin kudu maso gabas, Dr Ijeoma Arodiogbu ne ya bayyana hakan a wata hira da aka yi dashi a jaridar Punchng. Ya bayyana cewa gwamnonin jihohin Bayelsa, Rivers, Plateau, Kano, da daya daga cikin gwamnonin Abia ko na Enugu ne zasu koma jam'iyyar APC. Yace wannan ba jita-jita bane, tabbas ne kuma nan da watanni 2 kowa zai tabbatar da hakan. Hakan na zuwane kwanaki kadan bayan da Dr. Abdullahi Umar Ganduje ya sauka daga shugabancin jam'iyyar APC inda yace zai je ya kula da lafiyarsa.
Da Duminsa: Kasa da sati daya da saukar Ganduje daga shugaban APC, Gwamnan Kano, Abba Gida-Gida zai koma APC

Da Duminsa: Kasa da sati daya da saukar Ganduje daga shugaban APC, Gwamnan Kano, Abba Gida-Gida zai koma APC

Duk Labarai
Rahotannin da hutudole ke samu na cewa, Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf na shirin komawa jam'iyyar APC. Hakan na zuwane kwanaki kadan bayan saukar Dr. Abdullahi Umar Ganduje daga mukamin shugaban jam'iyyar. Mataimakin shugaban jam'iyyar APC reshen kudu maso gabas, Dr Ijeoma Arodiogbu ne ya bayyana hakan. Yace wannan magana bawai jita-jita bace tabbas ce lokaci kawa ake jira nan da watanni 2 kowa zai shaida. Dr Ijeoma Arodiogbu ya bayyana hakane a hirar da jaridar Punchng ta yi dashi inda yace sauran gwamnonin da zasu koma APC sune Gwamnonin jihohin Bayelsa, Rivers, da Plateau
Ni Peter Obi ya roka na taimaka masa ya zama mataimakin Atiku a zaben 2019>>Reno Omokri

Ni Peter Obi ya roka na taimaka masa ya zama mataimakin Atiku a zaben 2019>>Reno Omokri

Duk Labarai
Tsohon hadimin shugaban kasa, Goodluck Jonathan, Reno Omokri yace shine ya taimakawa Peter Obi ya zama mataimakin Atiku a zaben shekarar 2019. Ya bayyana hakane a wata hira da aka yi dashi, saidai magoya bayan Peter Obi sun karyatashi. Dalilin hakane ya ce zai bayyana shaidunsa. Ya dakko sakon Email da Peter Obi ya aika masa takardunsa. Yace Peter Obi yayi ta kiranshi dan ganin ya taimaka masa ya zama mataimakin Atiku inda har ta kai ga ya daina daukar wayarsa. Yace Atiku yace masa a wancan lokacin ya samo masa mutum me nagarta daga yankun kudu wanda zai zamar masa mataimaki. https://twitter.com/renoomokri/status/1939406025230254183?t=SKUyQdI7E5oCOCiaiCizIA&s=19 Yace kuma akwai mutane 2 da suka fi Peter Obi cancanta amma saboda yana girmama mutumin da ya hadashi ...
Ba sai kun sha Kwàyà ba zaku iya aiki>>Hukumar Sojojin Najeriya ta gargadi kananan sojojin

Ba sai kun sha Kwàyà ba zaku iya aiki>>Hukumar Sojojin Najeriya ta gargadi kananan sojojin

Duk Labarai
Hukumar sojojin Najeriya ta gargadi kananan sojoji cewa, ba sai sun sha kwaya ba zasu iya aiki yanda ya kamata. Kwamandan rundunar sojojin Najeriya ta 17 dake jihar Katsina, B.O. Omopariola ne ya bayyana haka a yayin wani tron karawa juna sani da aka gudanarwa sojojin kan matsalar tsaro. Jami'an hukumar yaki da safarar miyagun Kwàyòyì NDLEA sun halarci taron inda suka wayarwa da sojojin kai game da hadarin ta'ammuli da miyagun kwayoyin. B.O. Omopariola ya bayyana cewa bai yadda sai soja ya sha kwaya sannan zai iya aiki ba, yace sun yaki 'yan ta'dda sosai amma babu sojan da yayi amfani da kwaya a lokacin. Yace dan haka kada wani ya kawo mai maganar sai an sha kwaya sannan za'a iya aiki.
Da Duminsa: Gwamnan Filato ya tona asirin wadanda suka kirkiri matsalar tsaro a Najeriya

Da Duminsa: Gwamnan Filato ya tona asirin wadanda suka kirkiri matsalar tsaro a Najeriya

Duk Labarai
Gwamnan jihar Filato, Caleb Mutfwang ya bayyana cewa manyan mutane masu fada aji a kasarnan ne suka kirkiri matsalar tsaro a Najeriya. Ya bayyana hakane a wajan wani taro inda aka tattauna matsalar tsaro a jihar Filato ranar Laraba inda ya zargi masu fada aji da kawo matsalar tsaro a jiharsa. Yace wadanda suka kirkiri matsalar zasu iya magance matsalar tsaron idan suka ga dama. Yace idan irin wadannan manyan mutanen suka hada kai dan jagorancin mutane ta hanyar da bata kamata ba, za'a ci gaba da fuskantar matsalar tsaro duk shekara. Yace masu fada ajinne ke kara ruruta wutar rikicin ta hanyar zuga mutane akan ci gaba da rikicin. Ya jawo hankalin cewa, masu fada aji ya kamata suna karfaa zaman lafiya ne tsakanin al'umma.
Sabbin Motocin jigilar man fetur da muka kawo zasu samar da ayyuka 15000>>Dangote

Sabbin Motocin jigilar man fetur da muka kawo zasu samar da ayyuka 15000>>Dangote

Duk Labarai
Matatar man fetur ta Dangote tace sabbin motocin jigilar man fetur data kawo guda 4000 zasu samar da ayyukan yi na kai tsaye guda 15,000. Matatar tace mutanen da zasu samu ayyukan sun hada da Direbobi da manajoji da sauransu. Matatar man fetur din tace ta kashe Naira Biliyan 720 wajan sayo wadannan motocin jigilar man fetur din. Matatar tace zata kashw naira Tiriliyan N1.07 waja rabon man fetur din a shekara. Tace nan da 15 ga watan Augusta zata fara raba man zuwa gidajen man fetur da manyan masana'antu da sauran manyan masu amfani da man fetur a fadin Najeriya. Matatar tace wannan tsari zai amfani kananan masana'antu guda miliyan 42.