Tuesday, December 16
Shadow
Me magana da yawun shugaban kasa ya nemi a zartar da hukuncin ķķìsà kan matashiya ‘yar bautar kasa data soki Gwammatin Tinubu

Me magana da yawun shugaban kasa ya nemi a zartar da hukuncin ķķìsà kan matashiya ‘yar bautar kasa data soki Gwammatin Tinubu

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa, me taimakawa shugaban kasa kan yada labarai, Temitope Ajayi ya nemi a zartar da hukuncin kisa kan matashiya Ushie Uguamaye saboda sukar da tawa shugaba Bola Ahmad Tinubu. Kafar peoplesgazette ce ta wallafa cewa Temitope Ajayi ya nemi a yankewa Ushie hukuncin kisa saboda yace a zartar mata hukunci mafi tsanani da hukumar bautar kasa ta NYSC ta tanadar. Saidai a bayaninsa, Ajayi, ya bayyana cewa, shi ba haka yake nufi ba, an canja masa manufar bayaninsa ne dan cimma wani buri. Yace abinda yake nufi da zartarwa da Ushie hukunci mafi tsanani a dokar NYSC shine a koreta daga aikin bautar kasar, yace shi a iya saninsa wannan ne hukunci mafi tsanani a dokar NYSC ba hukuncin kisa ba. Lamarin Ushie ya dauki hankula sosai inda ciki hadda Atiku Abubakar, da Pet...
Gwamnatin Shugaban kasa, Donald Trump zata kulle gidan yada labarai na VOA

Gwamnatin Shugaban kasa, Donald Trump zata kulle gidan yada labarai na VOA

Duk Labarai
Rahotanni daga kasar Amurka sun bayyana cewa, shugaban kasar, Donald Trump yace zai kulle kafar yada labarai ta VOA. Dalili kuwa shine ana zargin kafar da rashin nuna goyon baya ga shugaba Trump. Shugaban VOA, Mike Abramowitz ya bayyana cewa, shi da ma'aikatansa, 1,300 duk an ce su tafi hutu kuma an dakatar da Albashinsu. Ya bayyana cewa, wannan na zuwane a yayin da kasashe irin su Iran, China da Rasha ke yada labaran karya game da kasar ta Amurka. Ana ganin dai wannan matakin kamar hanyace ta dakile aikin jarida da Shugaba Trump ya dauko.
Ji labarin Ushie Uguamaye, ‘Yar bautar kasa data tayarwa da gwamnatin Tarayya hankali saboda sukar Gwamnatin Tinubu, Saidai Atiku, da Peter Obi sun goyi bayanta

Ji labarin Ushie Uguamaye, ‘Yar bautar kasa data tayarwa da gwamnatin Tarayya hankali saboda sukar Gwamnatin Tinubu, Saidai Atiku, da Peter Obi sun goyi bayanta

Duk Labarai
Ƴan Najeriya na ta musayar yawu dangane da makomar Ushie Uguamaye mai yi wa ƙasa hidima mazauniyar birnin Legas, tun bayan da ta yi zargin fuskantar barazana sakamakon kalamanta da ta yi a shafinta na tiktok inda ta soki gwamnatin Bola Tinubu. Tuni dai jagororin adawa na Najeriya da kuma ƙungiyoyi masu rajin kare haƙƙin bil'adama suka nemi da hukumar yi wa ƙasa hidima ta NYSC ta tabbatar da cewa babu abin da ya samu Ushie Uguamaye. Ita dai hukumar ta NYSC ba ta ce uffan ba dangane da zargin barazanar da Ushie Uguamaye ta yi. Me Ushie Uguamaye ta faɗi? A wani bidiyo da ta wallafa a shafinta na tiktok ranar Asabar, Ushie Rita Uguamaye ta bayyana damuwa kan taɓarɓarewar tattalin arziƙi a Najeriya inda ta nuna takaicinta kan yadda jajircewa ke neman zama aikin banza. Ta kuma fit...
Kalli Bidiyon yanda Sojojin Najeriya suka lakadawa ma’aikatan wutar Lantarki dukan tsiya saboda yawan dauke musu wuta

Kalli Bidiyon yanda Sojojin Najeriya suka lakadawa ma’aikatan wutar Lantarki dukan tsiya saboda yawan dauke musu wuta

Duk Labarai
A dazu ne muka ji yanda sojoji suka sake zuwa Ofishin hukumar wutar lantarki ta jihar Legas inda suka lakadawa jami'an hukumar dukan kawo wuka. Lamarin ya dauki hankula musamman ganin ba'a dade ba hakan ta faru a baya. A wannan karin rahotanni sun ce sojojin sun dauki manyan ma'aikata biyu inda suka kaisu barikinsu suka lakada musu duka. Wannan bidiyon ya nuna yanda lamarin ya faru. Kalli bidiyon anan
Ji yanda Wani dan jarida yawa Sanata Godswill Akpabio Tonin Sillili inda ya bayyana dalilin da ya zama dole a kama shi a daure a gidan yari

Ji yanda Wani dan jarida yawa Sanata Godswill Akpabio Tonin Sillili inda ya bayyana dalilin da ya zama dole a kama shi a daure a gidan yari

Duk Labarai
Dan jarida kuma tsohon editan jaridar Daily Times newspaper me suna Chief Tola Adeniyi ya soki kasancewar Sanata Godswill Akpabio a matsayin kakakin majalisar Dattijai. Ya bayyana cewa, kamata yayi ace Sanata Akpabio na gidan yarine ba wai a majalisar dattijai ba. Yace Akpabio da masu hali irin nasa kamata yayi ace suna gidan yari, ya kara da cewa ka je ka duba zarge-zargen da akewa Sanata Akpabio inda ake zargin ya ci kudi Biliyan 44 da biliyan 90 da dai sauransu. Yace sannan kuma ga zargin lalata da sanata Natasha Akpoti ke masa. Yace abin kunyane ace irin wadannan mutanen ne akewa jiniya ana yawo dasu a kan totunanmu.
Ba neman izinin Komawa SDP na je yi wajan Buhari ba, najene in sanar dashi a matsayinsa na Uban gidana>>El-Rufai

Ba neman izinin Komawa SDP na je yi wajan Buhari ba, najene in sanar dashi a matsayinsa na Uban gidana>>El-Rufai

Duk Labarai
Tsohon Gwamnan jihar Kaduna, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai ya bayyana cewa, ba neman izinin komawa SDP ya je yi wajan tsohon shugaban kasa, Muhammadu Buhari ba. Yace ya jene ya sanar dashi a matsayinsa na uban gidansa a Siyasa. Tsohon Gwamnan ya bayyana hakane a shafinsa na sada zumunta inda yace wannan bayani ya dole yayishi saboda yanda ake ta samun rahotanni wanda ba daidai ba daga gidajen jaridu. Bayan komawar El-Rufai SDP kuma yace da sanin tsohon shugaban kasar, Muhammadu Buhari yayi hakan, Tsohon shugaban kasar ya fito yace har yanzu yana Jam'iyyar APC saboda ta bashi dama ya zama shugaban kasa har sau 2.
Yayin da suka rasa yanda zasu yi, kasar Nijar ta roki Najeriya ta taimaka mata da man fetur

Yayin da suka rasa yanda zasu yi, kasar Nijar ta roki Najeriya ta taimaka mata da man fetur

Duk Labarai
Kasar Nijar bayan nuna cewa ba ruwanta da Najeriya ta sakko kasa inda ta nemi Najeriyar ta taimaka mata da man fetur. Wahalar Man fetur ta yi yawa a kasar ta Nijar inda ake ganin dogayen layuka a gidajen mai sannan lamarin ya taba 'yan kasuwa da yawa kuma ya na son durkusar da harkar sufuri. Dalilin hakane Shugaban soja na kasar Nijar ya aiko da wakilansa da suka hada da ministan man fetur na kasar da wasu suka je Abuja suna neman a taimakesu da man fetur din. Tuni dai aka aika da tankokin man fetur 300 zywa Nijar din dan tallafa musu.
Na rasa wace irin matace Sanata Natasha Akpoti, ta kawo mana korafi, ba’a gama bincike ba ta tsallaka ta kai kara kotu, ba’a gama shari’a ba ta sake tsallakewa ta kai korafi majalisar Dinkin Duniya>>Sanata Godswill Akpabio

Na rasa wace irin matace Sanata Natasha Akpoti, ta kawo mana korafi, ba’a gama bincike ba ta tsallaka ta kai kara kotu, ba’a gama shari’a ba ta sake tsallakewa ta kai korafi majalisar Dinkin Duniya>>Sanata Godswill Akpabio

Duk Labarai
Kakakin majalisar dattijai, Sanata Godswill Akpabio ya koka da irin halayyar Sanata Natasha Akpoti inda yace bai san wane irin tunani gareta ba. Sanata Godswill Akpabio yace ta kawowa kwamitin da'a na majalisar dattijai korafi, ba'a gama bincike ba ta tafi ta kai kara kotu, can ma ba'a gama shari'a ba ta tafi ta kai korafi majalisar Dinkin Duniya. Sanata Godswill Akpabio yace irin wannan abun ne zai iya sawa a daina baiwa mata mukaman siyasa.
Bamu yadda da dawowar El-Rufai Jam’iyyar mu ba, yazo ne kawai ya cimma burinsa>>Kungiyar Matasan Jam’iyyar SDP

Bamu yadda da dawowar El-Rufai Jam’iyyar mu ba, yazo ne kawai ya cimma burinsa>>Kungiyar Matasan Jam’iyyar SDP

Duk Labarai
Kungiyar matasan Jam'iyyar SDP sun bayyana cewa basu yadda da komawar tsohon gwamnan Kaduna, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai Jam'iyyar ba. Kungiyar ta bakin shugabanta, Abdulsamad Bello ta bayyana cewa, El-Rufai kawai yana son samun damar da zai cimma burinsa ne a Jam'iyyar. Sun kara da cewa, abin takaici ne yanda Jam'iyyar ta baiwa El-Rufai dama aka tarbeshi hannu biyu-biyu ba tare da la'akarin hadarin da ke tattare dashi ba. Matasan sun ce karamin misali shine yanda El-Rufai da ga zuwansa gashi yana son yayi kaka gida a Jam'iyyar har yayi yunkurin tsike sakataren Jam'iyyar, Dr. Olu Agunloye daga mukaminsa. Kungiyar tace zata yaki duk wani yunkuri na neman mikawa El-Rufai Jam'iyyar inda suka gargadi shuwagabannin Jam'iyyar kada su aikata haka.