Saturday, May 2
Shadow
Yarbawan Arewa sun yiwa shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu alkawarin Kuri’u Miliyan 10 a zaben 2027

Yarbawan Arewa sun yiwa shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu alkawarin Kuri’u Miliyan 10 a zaben 2027

Duk Labarai
Kungiyar yarbawa magoya bayan shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu me suna (NOYAT) sun yiwa shugaban kasar Alkawarin samar masa da kuri'u Miliyan 10. Kungiyar a shekara 2022 ta shirya taro na musaman kan goyon bayan shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu a jihar Kaduna wanda ya samu halartar manyan mutane ciki hadda malaman addini. A sanarwar da kungiyar ta fitar ranar Laraba, ta sanar da cewa, tana jinjinawa shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu saboda nada Yazeed Shehu Danfulani shugaban hukumar inshora ta manoma ta kasa, (NAIC). Kungiyar a sanarwar wadda kakakinta, Mr. Seun Ogunyinka ya ftar tace nadin ya karfafa matasa sannan kuma 'yan Najeriya da dama sun ji dadi inda suka bayyana Danfulani a matsayin gwarzo wanda aka sanshi da aiki Tukuru.
Dukkan Alamu na nuni da cewa, kasar Amurka da Israyla na gaf da afkawa kasar Ìràn da yaki, Amurkar ta fara kwashe ‘yan kasarta daga ofisoshin jakadancin dake gabas ta tsakiya

Dukkan Alamu na nuni da cewa, kasar Amurka da Israyla na gaf da afkawa kasar Ìràn da yaki, Amurkar ta fara kwashe ‘yan kasarta daga ofisoshin jakadancin dake gabas ta tsakiya

Duk Labarai
Kasar Amurka ta bayar da umarnin kwashe ma'aikatan ta dake ofishin jakadancinta na kasar Iraqi inda ta bayyana cewa akwai fargabar tsaro. Hakanan rahotanni sun ce Amurkar ta na kwashe wakilanta daga kasar UAE Ana tsammanin haka shirine na Afkawa kasar Ìràn da yaki saboda hanata mallakar makamin kare dangi. Kasar Iran tace muddin Amurka ko Israyla suka kai mata hari, zata tabbatar ta kaiwa kadarorin kasar Amurkar dake yankin Gabas ta tsakiya hari. Shugaban Amurka, Donald Trump ya bayyana cewa, ba zasu bar Iran ta mallaki makamin kare dangi ba. Rahotanni sun ce kasar Iran ta ki baiwa Amurka hadin kai a tattaunawar neman sulhu dan karta mallaki makamin kare dangi.
Masu zanga-zanga sun shirya tsaf dan nunawa shugban kasa, Bola Ahmad Tinubu fushinsu a yau ranar Dimokradiyya

Masu zanga-zanga sun shirya tsaf dan nunawa shugban kasa, Bola Ahmad Tinubu fushinsu a yau ranar Dimokradiyya

Duk Labarai
Rahotanni sunce akwai artabu da dauki ba dadi da akw tsammanin zau faru a yau tsaanin masu zanga-zanga da jami'an tsaro a majalisar tarayya dake Abuja. Masu zanga-zangar ta ranar 'yanci shin shirya zanga-zangar a Abuja dama gurare 19 a fadin kasarnan. A yau ne ake sa ran shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu zai halarci majalisar tarayya dan karrama wasu 'yan majalisar sannan a canne zai gabatarwa da 'yan kasa jawabi. A baya dai, shugaban kasar ya so ya gabatar da jawabin ga 'yan kasa da safiyar Ranar Alhamis amma daga baya aka canja tsari aka ce sai ya je majalisar tarayya. Maau zanga-zangar sun ce zasu gabatar da kokensu ne game da matsalar matsim tattalin arzikin da talakawa ke ciki.
Karanta Jadawalin manyan gurare 7 da aka sakawa sunan shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu tun bayan da ya hau mulki

Karanta Jadawalin manyan gurare 7 da aka sakawa sunan shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu tun bayan da ya hau mulki

Duk Labarai
Tun daga 29 ga watan Mayu na shekarar 2023 bayan da shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya zama shugaban Najeriya, an sakawa manyan gurare na gwamnati guda 7 sunansa. Daga cikin abubuwan da aka sakawa sunan Shugaban kasar akwai tituna, Barikin sojoji, dakunan taro da sauransu. Wata kungiyar rajin kare hakkin bil'adama me suna (NEFGAD) ta bayyana hakan a matsayin abinda bai dace ba dan ya sabawa aikin gwamnati. Ga jadawalin gurare 7 da aka sakawa sunan shugaban kasar kamar haka: Babban Filin Jirgin sama na jihar Naija. A ranar March 10, 2024 ne gwamnan jihar Naija, Umar Bago ya sakawa babban filin sauka da tashin jiragen jihar dake Minna sunan shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu. Titun Abuja Southern Parkway. A ranar May 28, 2024 ne bayan kammala titin Abuja Southern Parkway...
Yanda na yi turin baro a kasar Ingila duk da cewa ni likita ne a Najeriya>>Inji Dr. Kelvin Alaneme 

Yanda na yi turin baro a kasar Ingila duk da cewa ni likita ne a Najeriya>>Inji Dr. Kelvin Alaneme 

Duk Labarai
Wani likitan Najeriya da ya koma da zama a kasar Ingila me suna, Dr. Kelvin Alaneme ya bayar da labarin yanda ya karkare da turin bari a kasar Ingila. Yace a shekarar 2019, ya jw kasar Ingila duk da shi likita ne a Najeriya amma bai samu lasisin yin aikin likitanci a kasar Ingilar ba. Yace haka suka hadu shi da wani abokinsa me suna Surya suka rika neman yanda zasu yi tare. Yace kudinsa na karewa kuma gashi yana bukatar ya mayar da iyalansa zuwa Ingila, yasan cewa idan bai samu aikin yi ba akwai matsala. Yace a haka wata rana ya kira Surya yace tunda dai aikin ofis ya ki samuwa su je su nemi koma wane irin aiki ne su yi. Yace haka suka rika bi shago-shago suna tabayar ko zasu samu aiki amma ana ce musu babu. Yace sun kusa kammala titin gaba daya sai suka shiga shagon wani...
Karanta Jadawalin yankunan Najeriya da aka fi samun yaran da basa zuwa makaranta

Karanta Jadawalin yankunan Najeriya da aka fi samun yaran da basa zuwa makaranta

Duk Labarai
An bayyana yankunan da suka fi yawan yaran da basa zuwa makaranta a Najeriya. Kafar Statisense da UNICEF ne suka bayyana wadannan bayanai kamar haka: North West — 8.04 millionNorth East — 5.06 millionNorth Central — 2.12 millionSouth West — 1.15 millionSouth South — 769KSouth East — 664K Northern Nigeria — 15.23 millionSouthern Nigeria — 2.58 million
An bayyana yankunan da suka fi yin jima’i ba tare da Kwandon ko Kwaroron robaba a Najeriya

An bayyana yankunan da suka fi yin jima’i ba tare da Kwandon ko Kwaroron robaba a Najeriya

Duk Labarai
Wani bincike ya bayyana yankunan da suka fi yin Jima'i ba tare da Kwaroron ribaba. Yankuman sune kamar haka: North East — 70.6%South South — 67.0%North West — 64.4%South West — 63.1%South East — 61.6%North Central — 59.9% Sai kuma yankunan da suka fi yin jima'i da mutane daban-daban. Suma sune kamar haka: North East — 72.8%South South — 68.7%South West — 68.2%North Central — 62.9%South East — 65.6%North West — **** Kafar Statisense ce ta gudanar da wannan bincike.
Da Duduminsa: Shugaba Tinubu ya fasa jawabin da zai wa ‘yan Najeriya a gobe ranar ‘yanci, ji dalili

Da Duduminsa: Shugaba Tinubu ya fasa jawabin da zai wa ‘yan Najeriya a gobe ranar ‘yanci, ji dalili

Duk Labarai
Rahotanni daga fadar shugaban kasa na cewa, shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya fasa jawabin da ya shirya yiwa 'yan Najeriya da safiyar ranar 'yanci. Rahotan yace, maimakon haka, shugaban zai yiwa 'yan Najeriya jawabi ne daga zauren majalisar tarayya. Shugaba Tinubu zai halarci zauren majalisar tarayya dan baiwa wasu 'yan majalisar kyautar girmamawa.
Bayan Kammala aikin Hajji, Saudiyya ta sanar da buɗe ƙofarta ga masu son zuwa Umarah

Bayan Kammala aikin Hajji, Saudiyya ta sanar da buɗe ƙofarta ga masu son zuwa Umarah

Duk Labarai
Ma’aikatar Hajji da Umarah ta ƙasar Saudiyya ta sanar da buɗe ƙofarta ga masu son zuwa aikin Umarah na shekarar Hijira ta 1447, wanda zai fara daga ranar Talata, 10 ga Yuni. Ma’aikatar ta tabbatar da cewa za a fara bayar da takardar izinin Umarah ga ƴan ƙasashen waje daga yau Laraba, 11 ga watan Yuni, ta manhajar "Nusuk". Saudiyya ta dakatar da bayar da izinin aikin Umarah a watan Afrilun 2025, sannan ta ayyana 29 ga Afrilu a matsayin rana ta ƙarshe da masu Umarah za su bar ƙasar, gabanin aikin Hajjin shekarar 2025. Mutane sama da miliyan ɗaya da dubu ɗari shida ne suka gudanar da aikin hajjin bana a ƙasar Saudiyya. Ma’aikatar ta bayyana cewa an fara shirye-shirye tare da haɗin gwiwa da hukumomi da masu ruwa da tsaki, domin tabbatar da saukin aiwatar da dukkan matakai da kuma c...