Saturday, May 2
Shadow
Tsohon Ministan Sufuri, Rotimi Amaechi yayi bayani dalla-dalla dalilin da yasa yake son su hada kai dan kayar da Shugaba Tinubu

Tsohon Ministan Sufuri, Rotimi Amaechi yayi bayani dalla-dalla dalilin da yasa yake son su hada kai dan kayar da Shugaba Tinubu

Duk Labarai
Tsohon ministan sufurin Najeriya, Rotimi Amaechi ya ce a shirye yake don shiga ƙawancen ƴan hamayya a ƙasar domin ƙalubalantar Shugaba Bola Tinubu. Amaechi - wanda ɗan jam'iyyar APC ne - ya nuna damuwa kan abin da ya ƙira ƙuncin rayuwa da ƙasar ne ciki. A wata hira da BBC, tsohon gwamnan na jihar Rivers ya ce suna ƙoƙarin samar da haɗakar siyasar da za ta samar da sauyi a ƙasar. Amaechi ya ce bai cire tsammanin yin takarar shugaban ƙasa ba, illa lokaci ne kawai zai tantance. Kalaman Amaechi na zuwa ƙasa da wata ɗaya bayan jagororin jam'iyyar APC sun amince da Bola Tinubu a matsayin "ɗan takara ɗaya tilo" a zaɓen 2027. Sai dai tsohon ministan ya ce har yanzu yanan nan a jam'iyyar APC, kuma ''bai zama dole sai ka goyi bayan gwamnati ba, don kawai kana APC. ''Idan gwamnati t...
Za a kai ƙarar mai taimaka wa gwamnan Zamfara kan alaƙanta matawalle da ƴànbìngìdà

Za a kai ƙarar mai taimaka wa gwamnan Zamfara kan alaƙanta matawalle da ƴànbìngìdà

Duk Labarai
Jam’iyyar APC reshen Jihar Zamfara ta bayyana aniyar ɗaukar matakin shari’a kan Mustapha Jafaru Kaura, mai taimaka wa gwamnan jihar, Dauda Lawal, kan yada labarai bisa zargin yi wa shugabannin jam’iyyar ƙazafi tare da alaƙantasu da ‘yanbindiga da kuma garkuwa da mutane a jihar. A cewar wata sanarwa da sakataren yaɗa labaran APC na jihar, Yusuf Idris Gusau ya fitar bayan taron gaggawa na kwamitin gudanarwar jam'iyyar da aka gudanar a Gusau. Jam’iyyar ta bayyana kalaman jami'in na gwamnatin Zamfara, Jafaru Kaura a matsayin “kalaman harzuƙa jama'a da ɓata suna.” APC ta ce Mustapha Kaura ya yi iƙirarin cewa Bello Mohammed Matawalle, ƙaramin ministan tsaro kuma tsohon gwamnan Zamfara—ya riƙa haɗa baki da ƴanbindiga a lokacin mulkinsa. Sanarwar ta ce Kaura a wata hira da aka yi da sh...
An kàshè mutane 20 a sabbin hàrè-hàrèn da aka kai jihar Filato

An kàshè mutane 20 a sabbin hàrè-hàrèn da aka kai jihar Filato

Duk Labarai
Hare-haren da aka kai a Jihar Filato sun hallaka aƙalla mutum 20 a wannan makon, in ji majiyoyin gwamnati da ƙungiyoyin agaji a ranar Laraba. Wannan lamari na daga cikin sabbin hare-hare da tashin hankali da ke ci gaba da faruwa a yankin. Hare-hare daban-daban guda uku da suka faru a yankin ƙaramar hukumar Mangu a ranar Litinin da Talata, sun biyo bayan jerin hare-hare da ramuwar gayya da ake kyautata zaton sun fara ne yayin da mutane ke aikin haƙar ma’adinai a yankin da ke da arzikin Tin, a cewar shugaban ƙaramar hukumar, Emmanuel Bala, da ya shaida wa Kamfanin dillancin labarai na AFP. "Makiyayan Fulani Musulmai masu yawo da dabbobi sun daɗe suna samun saɓani da manoma da suke zauna a Jihar Filato — waɗanda mafi yawansu Kiristoci ne — kan rikicin mallakar fili da albarkatun ƙasa...
Alummar garin Mokwa na fargabar ɓarkewar cùtùkà saboda gàwàrwàkìn da ba a gano ba

Alummar garin Mokwa na fargabar ɓarkewar cùtùkà saboda gàwàrwàkìn da ba a gano ba

Duk Labarai
Aƙalla makonni biyu da afkuwar ambaliyar ruwan da ta hallaka mutane tare da share gidaje masu dimbin yawa a garin Mokwa na jihar Neja, jama'ar yankin na kokawa kan yadda aka soma jin warin gawarwakin mutanen da har kawo yanzu ba a kai ga ganowa ba. Jama’a dai na ci gaba da bayyana cewa warin na iya haifar da matsala ga lafiya, musamman ana fargabar barkewar kwalara kasancewar da dama daga rijiyoyin jama’a da suke samun ruwan sha sun rufta. Daga cikin wadanda BBC ta zanta da su, sun ce tun daga ranar asabar ta karshen makon daya gabata suka soma jin warin gawarwakin. Sai dai wasu mazauna garin na Mokwa sun ce a yanzu dai fargabar da ake da ita ta ɗan ragu bayan da aka soma yin feshin magani a wasu wurare. Sun kuma ce Unicef ta bayar da wasu magunguna da ake sawa cikin ruwan da z...
A karin farko a Tarihinta, Kasar Uzbekistan ta zo gasar cin kofin Duniya, domin Murna, An baiwa kowace dan kwallon kasar kyautar mota

A karin farko a Tarihinta, Kasar Uzbekistan ta zo gasar cin kofin Duniya, domin Murna, An baiwa kowace dan kwallon kasar kyautar mota

Duk Labarai
{"remix_data":[],"remix_entry_point":"challenges","source_tags":[],"origin":"unknown","total_draw_time":0,"total_draw_actions":0,"layers_used":0,"brushes_used":0,"photos_added":0,"total_editor_actions":{},"tools_used":{},"is_sticker":false,"edited_since_last_sticker_save":false,"containsFTESticker":false} Kasar Uzbekistan sun je gasar cin kofin Duniya a karin farko a tarihinsu. Duka 'yan wasan kasar an basu kyautar motoci bayan sun yi nasara akan kasar Qatar a wasan karshe da suka buga. Gidan Uzbekistan aka je kuma sune suka ci Qatar Kwallaye 3-0. Bayan kammala wasan, an kawo motocin BYD guda 40 inda aka baiwa kowane dan kwallon kasar makullin sabuwar mota.
Zan iya mùtùwà a kan APC, in ji tsohon Gwamnan Abia, Uzor Kalu

Zan iya mùtùwà a kan APC, in ji tsohon Gwamnan Abia, Uzor Kalu

Duk Labarai
Tsohon Gwamnan Jihar Abia, Orji Uzor Kalu, ya sake jaddada cewa a shirye ya ke ya ba da ransa akan jam’iyyar APC, musamman a jihar Abia. Ya bayyana haka ne a hirarsa da manema labarai a garinsu na Igbere, Jihar Abia. Da aka tambaye shi ko APC na da wata dama ta kayar da jam’iyyar Labour Party (LP) a zaben 2027 a jihar Abia, Kalu wanda ke wakiltar Abia ta Arewa a Majalisar Dattawa, ya ce shi da sauran magoya bayan APC za su yi aiki tukuru domin nasarar shugaban kasa a jihar. Ya ce; “APC na da karfi a Abia. Kamar yadda na fada a wata hira, wla shirye nake in ba da raina saboda jam’iyyar. Ni mamba ne na APC kuma mai tsayawa kan gaskiyar jam’iyyar. Ni cikakken dan APC ne. Shi ya sa APC ke da karfi a Abia ta Arewa. “Jam’iyyarmu za ta yi aiki tukuru domin ganin shugaban kasa ya yi na...
Gwamnatin tarayya ta soke faretin bikin ranar dimokuraɗiyya

Gwamnatin tarayya ta soke faretin bikin ranar dimokuraɗiyya

Duk Labarai
Gwamnatin Tarayya ta soke faretin sojoji da ake yi don tunawa da Ranar Dimokuraɗiyya ta shekara-shekara, wadda za a gudanar da bikin ta a ranar Alhamis, 12 ga watan Yuni a matsayin cika shekara 26 da dimokuraɗiyya ta dawo Najeriya. Bayanan da Kwamitin Harkokin Bikin Ranar Dimokuraɗiyya na Ma’aikatu da dama ya fitar sun nuna cewa Shugaba Bola Tinubu zai yi jawabi ga al’ummar ƙasa baki ɗaya da misalin ƙarfe 7 na safe ranar Alhamis, ba tare da an gudanar da faretin Ranar Dimokuraɗiyya kamar yadda aka saba a baya ba. Maimaikon faretin, Shugaba Tinubu zai halarci zaman haɗin gwiwa na musamman da za a gudanar a Majalisar Tarayya da ƙarfe 12 na rana. Ana sa ran wannan zaman haɗin gwiwa zai ƙunshi jawaban da suka shafi halin da ƙasa ke ciki, tunawa da tafiyar dimokuraɗiyyar Najeriya, da k...
Natasha: Kotun Ɗaukaka Ƙara ta ci tarar Akpabio Naira dubu ɗari

Natasha: Kotun Ɗaukaka Ƙara ta ci tarar Akpabio Naira dubu ɗari

Duk Labarai
Kotun daukaka kara a Abuja ta yi watsi da bukatu guda biyu da Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Godswill Akpabio, ya shigar, tare da yanke masa hukuncin biyan tara na naira 100,000. Kwamitin alkalai uku na kotun, wanda Mai Shari’a Hamman Barka ke jagoranta, ne ya yanke hukuncin a ranar 21 ga Mayu, 2025, bayan Akpabio ya nemi a janye karar da ya shigar. Kotun ta kuma tabbatar da sahihancin kwafin hukuncin. Bukatun da aka yi watsi da su an shigar da su ne a ranar 3 ga Maris, 2025, da kuma 25 ga Maris, 2025, kuma suna dauke da lambar shari’a CV/395/M1/2025 da CV/395/M2/2025, inda Akpabio ya kasance mai daukaka kara.
Bisa satar Naira miliyan 360, kotu ta yanke wa wani mutum hukuncin ɗaurin shekaru 74 a gidan yari

Bisa satar Naira miliyan 360, kotu ta yanke wa wani mutum hukuncin ɗaurin shekaru 74 a gidan yari

Duk Labarai
Wata babbar kotu da ke Ajah, a jihar Lagos, ta yanke wa Chukwudi Okonkwo Goodness, hukuncin daurin shekaru 74 a gidan yari bisa laifin satar Naira miliyan 360 da kuma bayar da takardun cirar kudi a asusun bankin da babu kuɗi a cikin sa. An gurfanar da Goodness ne a shekarar 2016 bisa tuhuma 33 da hukumar EFCC ta shigar. An ce ya karkatar da kuɗin ne daga wani mutum mai suna Henry Nnadike a Ikeja tsakanin watan Yuni da Yuli, 2015. Bayan shari’ar da ta ɗauki tsawon shekaru tara, mai shari’a Josephine Oyefeso ta same shi da laifi a kan tuhume-tuhume 32. Bayan haka an yanke masa hukuncin ɗaurin shekaru bakwai a kan tuhuma ta sata, sannan shekaru biyu-biyu a kowace tuhuma daga cikin sauran tuhume-tuhume da suka shafi bayar da katin cirar kudi a asusun da babu kuɗi a cikin sa. Haka z...
Bincike: Karanta Jadawalin jihohin da aka fi samun matan aure na aikata Zìnà, ‘yan mata ma na lalata, Rahoton yace babu irin wadannan matan ko daya a jihohin Jigawa, Katsina da Kebbi sannan Kuma jihar Taraba ce ta daya a Arewa wajan aikata wannan masha’a

Bincike: Karanta Jadawalin jihohin da aka fi samun matan aure na aikata Zìnà, ‘yan mata ma na lalata, Rahoton yace babu irin wadannan matan ko daya a jihohin Jigawa, Katsina da Kebbi sannan Kuma jihar Taraba ce ta daya a Arewa wajan aikata wannan masha’a

Duk Labarai
Wani rahoto daga kafar TheCable ya bayyana jihohin da aka fi samun matan aure da 'yan mata na aikata Zina da yawaitar karuwai. Rahoton yace an yi bincikene a kan 'yan mata masu shekaru tsakanin 15 zuwa 49. Rahoton yace a jihohin Jigawa, Katsina da Kebbi babu irin wadannan mata: Bayelsa: 28.5% Cross River: 23.9% Rivers: 23% Abia: 21.4% Delta: 22.1% Enugu: 20.3% Akwa-Ibom: 20.2% Edo: 20.1% Ondo: 19.9% Taraba: 19.9% Ekiti: 18.3% Benue: 16.8% Imo: 16.1% Lagos: 15.7% Osun: 15.2% Anambra: 14.9% FCT: 13.8% Plateau: 13% Kwara: 12.3% Oyo: 12.2% Ogun: 11.3% Kogi: 10.2% Nasarawa: 9.2% Ebonyi: 6.6% Adamawa: 5.6% Bauchi: 2.5% Gombe: 1.8% Kaduna: 1.7% Borno: 1.6% Niger: 1% Kano: 0.5% Zamfara: 0.5% S...