Monday, April 6
Shadow
Gwamna Bago ya janye matakin da ya ɗauka akan samari masu tara gashin dada a Neja

Gwamna Bago ya janye matakin da ya ɗauka akan samari masu tara gashin dada a Neja

Duk Labarai
Gwamna Bago ya janye matakin da ya ɗauka akan samari masu tara gashin dada a Neja. Gwamnan Jihar Neja, Umar Bago, ya janye umarninsa na baya da ya bayar ga jami’an tsaro da su kama masu gashin dada da maza masu Kitso a Minna, babban birnin jihar. Bago, yayin da yake magana a wani taron tsaro tare da masu ruwa da tsaki a gidan gwamnati ranar Talata, ya umarci jami’an tsaro da su yanke gashin dada na mutanen da aka kama tare da cin tarar kudi. Ya ce: “Duk wanda kuka gani da Gashin Dada, ku kama shi, ku yanke masa gashi, sannan ku ci shi tara. “Babu wanda zai rika yawo da irin wannan gashi a cikin Minna. Na riga na ba da umarni ga jami’an tsaro,” in ji gwamnan. Sai dai a ranar Laraba, gwamnan ya janye wannan umarni bayan ya fuskanci suka daga 'yan Najeriya da dama. Yayin...
Kalli Bidiyo: Wata Sabuwar Masifa ta Shigo kafafen sada zumuntar Arewa inda ake cin zarafin malamai ta hanyar Amfani da AI asa su yi rawa

Kalli Bidiyo: Wata Sabuwar Masifa ta Shigo kafafen sada zumuntar Arewa inda ake cin zarafin malamai ta hanyar Amfani da AI asa su yi rawa

Duk Labarai
Wata sabuwar masifa da ta shigo kafafen sada zumuntar Arewa itace ta amfani da wani AI ana saka hotunan malamai ana sawa su yi rawa. Wannan AI a baya 'yan siyasa kawai akewa amfani dashi amma yanzu lamarin ya kai har kan malamai. https://www.tiktok.com/@sanusi_lauwali/video/7494342086968462647?_t=ZM-8vmO2enRDGw&_r=1 Wasu daga cikin Malam da muka ci karo an yi Amfani da wannan AI din an sa sun yi rawa sun hada da Marigayi Shaikh Jafar Adam, da Sheikh Bala Lau da Sheikh Maqari. https://www.tiktok.com/@sanusi_lauwali/video/7495429012479659319?_t=ZM-8vmO9SppUg9&_r=1 Wani abin takaici ma shine lamarin ya koma gasa tsakanin matasa mabiya akidu, idan wannan ta saka malamin wannan akida rawa, sai shima wancan ya rama. https://www.tiktok.com/@sanusi_lauwali/video/7494...
Kalli Bidiyon mummunar girgizar kasar data faru a kasar Turkiyya, mutane na ta gudun ceton rai

Kalli Bidiyon mummunar girgizar kasar data faru a kasar Turkiyya, mutane na ta gudun ceton rai

Duk Labarai
Aƙalla mutane 151 ne suka samu raunuka bayan sun durgo daga dogayen gine-gine saboda tsoron da girgizar ƙasa ta haifar, a cewar ofishin gwamnan Istanbul. https://www.tiktok.com/@live_news00/video/7496509730362281238?_t=ZM-8vmJNkmOYiL&_r=1 Ofishin ya kuma wallafa a shafinsa na X, cewa ba a samu asarar rayuka ba, kuma babu wani gini da mutane ke zaune a ciki da ya ruguje. Sai dai wani gini wanda babu kowa a ciki ya ruguje sakamakon girgizar ƙasar. https://twitter.com/The_NewArab/status/1915025667365683236?t=7ep6E-k1HezvWfbB4qwjPQ&s=19 Ministan ilimi na Turkiyya, Yusuf Tekin ya sanar da cewa za a rufe makarantu na kwana biyu Alhamis da Juma'a. Aƙalla an samu girgiza sau 51 a birnin a ranar Laraba, inda mafi girmansu ya kai ƙarfin maki 6.2, wanda ya shafi Istambul...
Akwai ƴanƙasar waje da ke kai hari a Benue – Alia

Akwai ƴanƙasar waje da ke kai hari a Benue – Alia

Duk Labarai
Gwamnan jihar Benue da ke tsakiyar Najeriya, Hyacinth Alia ya yi zargi cewa maharan da suka kai hari jihar ba ƴan Najeriya ba ne. Gwamnan ya faɗi hakan ne a wani shirin gidan talbijin na Channels, inda ya ce maharan na magana ne da wata irin Hausa da Fulatanci wanda ba irinsu ake yi a ƙasar ba. "Waɗannan mutanen sun zo ne a shirye da makamansu da bindigogi ƙirar AK-47 da 49. Kuma ba su yi kama da ƴan Najeriya ba, ba sa magana kamar yadda muke yi, Hausarsu ba irin ta mu ba ce. " Inda ya ƙara da cewa daga bayanan sirrin da suka samu daga mazauna yankunan da aka kai hare-hare, ya nuna cewa maharan ƴanƙsar waje ne. Hakan na zuwa ne bayan wata ziyarar nuna alhini da mai baiwa shugaban Najeriya shawara kan harkokin tsaro, Nuhu Ribadu ya kai jihar. Inda ya bai wa al'umomin jihar ta...
Gwamnatin Kaduna ta ƙwace gidajen da El-Rufa’i ya sayar

Gwamnatin Kaduna ta ƙwace gidajen da El-Rufa’i ya sayar

Duk Labarai
Gwamnan jihar Kaduna da ke arewacin Najeriya, Uba Sani ya bayar da umarnin ƙwace gidaje da filayen da tsohuwar gwamnatin da ta shuɗe ta Malam Nasiru El-Rufa'i ta sayar a jihar. Gidajen da filayen da aka ƙwacen sun haɗa da waɗanda tsohon gwamnan ya sayar a kwalejin Queen Amina da ke Kaduna da kwalejin Alhuda-huda da kwalejin Government Commercial da ke Zaria. Umarnin na ƙunshe ne a wata sanarwar da aka fitar, a ranar Talata da daddare, mai ɗauke da sa hannun sakataren gwamnatin jihar, Dr AbdulKadir Mu’azu Meyere. Sanarwar ta bayyana cewa an ƙwace gidajen da filayen ne saboda amfanin al'umma. Sai dai an jima ana takun saƙa tsakanin gwamna Uba Sani mai ci yanzu, da kuma wanda ya gada, Malam Nasir El-Rufa'i.