Sunday, May 3
Shadow
A yau ne ake sa ran kasar Amurka zata fitar da bayanai na zargin shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu da safarar miyagun Kwàyòyì, Saidai fadar shugaban kasa da APC sun ce wannan ba wani abu bane, Duk abinda ya faru kamin Tinubu ya zama shugaban kasa ba’a sakashi a lissafi

A yau ne ake sa ran kasar Amurka zata fitar da bayanai na zargin shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu da safarar miyagun Kwàyòyì, Saidai fadar shugaban kasa da APC sun ce wannan ba wani abu bane, Duk abinda ya faru kamin Tinubu ya zama shugaban kasa ba’a sakashi a lissafi

Duk Labarai
A yau ne ake sa ran hukumomin kasar Amurka na FBI zasu saki bayanai akan zargin shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu da safarar miyagun kwayoyi a Birnin Chicago na kasar. Ana zargin Tinubu da asu mutane 3 Lee Andrew Edwards, Mueez Akande, da Abiodun Agbele a shekarun 1990 sun yi safarar miyagun Kwayoyi wanda shari'ar take kan Gudana. Lauyoyi da musamman 'yan Adawar shugaban kasar na neman a saki bayanai game da wannan binciken dan a san wanene shugaban kasar. A baya ba'a samu hadin kan hukumomin kasar Amurkar ba game da sakin bayanan, amma a yanzu sun amince kuma a yau, Juma'a ne ake sa ran sakin wadannan bayanan. Saidai fadar shugaban kasa ta bakin me magana da yawun shugaban kasar, Bayo Onanuga tace tabbas lauyoyi na kan binciken wannan magana. Saidai fadar tace bayanan ko da ...
Kalli Hoton Sabon Salon Rashin Imani  yanda ‘yan Bìndìgà suka fara yankewa wanda suka yi garkuwa dasu hannu idan ba’a kai kudin fànsà ba

Kalli Hoton Sabon Salon Rashin Imani yanda ‘yan Bìndìgà suka fara yankewa wanda suka yi garkuwa dasu hannu idan ba’a kai kudin fànsà ba

Duk Labarai
'Yan Bindiga dake garkuwa da mutane dan neman kudin fansa sun fito da wata sabuwar azabtar da mutanen sa suka yi garkuwa dasu. A yanzu an fara ganin 'yan Bindigar na yankewa mutane hannu su sakosu idan ba'a kai musu kudin fansa ba. Lamarin ya farune a karamar hukumar Yagba West dake jihar Kogi. Mutane 3 suka yiwa wannan azaba.
Gwamnatin Tinubu ta yi ikirarin cewa daga Saudiyya sai Nigeria wajan saurin habakar tattalin arziki amma an gano Karyane wannan ikirarin na gwamnati

Gwamnatin Tinubu ta yi ikirarin cewa daga Saudiyya sai Nigeria wajan saurin habakar tattalin arziki amma an gano Karyane wannan ikirarin na gwamnati

Duk Labarai
Gwamnatin tarayya ta yi ikirarin cewa Najeriya ce ta hudu a bayan kasashen India, China da Saudi Arabia wajan saurin habakar tattalin Arziki. Saidai an gano wannan ikirarin ba gaskiya bane. Gwamnatin Ta yi ikirarin cewa wannan bayanai sun fito ne daga hukumar bayar da lamuni ta Duniya IMF. Saidai bincike ya bayyana cewa Najeriya ta 37 ce ba ta 4 ba a jerin kasashen masu saurin habakar tattalin arziki.
Mu a Arewa muna sayarwa da ‘yan Kudu gidaje da Filaye amma mu basa sayar mana a yankinsu>>Kungiyar ACF ta koka

Mu a Arewa muna sayarwa da ‘yan Kudu gidaje da Filaye amma mu basa sayar mana a yankinsu>>Kungiyar ACF ta koka

Duk Labarai
Kungiyar Tuntuba ta Arewa me suna ACF ta bayyana cewa, abin takaici ne ya da 'yan Arewa a kudancin Najeriya ba'a sayar musu da gidaje da Filaye. Amma nan a Arewa 'yan kudu na ta mallakar gidaje da filaye. Shugaban kwamitin amintattu na kungiyar, Alhaji Bashir Dalhatu ne yayi wannan kirafi inda yace ya kamata a jihohi 19 na Arewa a fito da sabon tsarin mallakar fili da gida dan magance wannan matsala. Yace musamman a jihohin Inyamurai basa sayarwa da 'yan Arewa fili. Yace idan ba'a tashi tsaye aka magance wannan matsala ba, muna ji muna gani zamu sama bamu da fili ko gida a garuruwan mu duk baki sun saye.
Shugaban Kungiyoyin da suka kai korafi a Abinciki tsohon Shugaban NNPCL, Mele Kolo Kyari ya janye bukatar binciken saidai abokan Gwagwarmayarsa sun ce basu tare dashi saboda an sallameshi ne

Shugaban Kungiyoyin da suka kai korafi a Abinciki tsohon Shugaban NNPCL, Mele Kolo Kyari ya janye bukatar binciken saidai abokan Gwagwarmayarsa sun ce basu tare dashi saboda an sallameshi ne

Duk Labarai
Shugaban Kungiyoyin gwagwarmaya da suka hada kai suka kai bukatar a binciki tsohon shugaban kamfanin man fetur na kasa, NNPCL, Mele Kolo Kyari ya je ya janye bukatar binciken. Kungiyoyin sun ce basa tare da shugaban nasu me suna Kabir Matazu. A wata sanarwa da sakataren kungiyoyin me suna Moses Okino ya fitar, yace Matazu ya yaudaresu da cin amanarsu. Kungiyar tace dama can akwai wasu na hannun damar Mele Kolo Kyari dake ta son su hana binciken me gidan nasu. Yace dan haka abinda Matazu yayi ba da yawun kungiya yayi ba yayi ne shi kadai bisa radin kansa. Yace Matazu bai tuntubesu ba dan haka suna kyautata zaton kudi aka bashi.
Gwamnonin arewa maso gabashin Najeriya na taro kan tsaro a yankin

Gwamnonin arewa maso gabashin Najeriya na taro kan tsaro a yankin

Duk Labarai
A ranar Litinin ɗin nan ne gwamnonin shiyyar arewa maso gabashin Najeriya suke taro a birnin Damaturu babban birnin Jihar Yobe kan matsalolin da yankin ke fama da su. Taron na zuwa a daidai lokacin da yankin ke fama da sabin hare-haren mayakan Boko Haram. Masana da al'ummar yankin na cewa dama ce gwamnonin suka samu domin tattauna yadda za a shawo kan matsalar tsaro da ke addabar yankin. A ranar Talata ne dai ƙungiyar ISWAP ta ɗauki alhakin kai wani harin bam da ya yi sanadiyyar mutuwar mutum 26 a Rann a jihar Borno.
Masu gudanarwa na jami’o’in Najeriya sun sace Naira Biliyan 71.2 daga cikin kudaden da aka bayar a baiwa daliban jami’o’in bashi

Masu gudanarwa na jami’o’in Najeriya sun sace Naira Biliyan 71.2 daga cikin kudaden da aka bayar a baiwa daliban jami’o’in bashi

Duk Labarai
Hukumar da ke yaƙi da masu yi wa ƙasar almundahana, ICPC ta ƙaddamar da wani bincike kan zargin zabtare wa ɗaliban da gwamnati ta bai wa bashin karatu da ake kira NELFUND da makarantu da jami'o'i ke yi. Hukumar ta ICPC wadda ta wallafa hakan a shafinta na X, ta ce w annan dai ya biyo bayan rahotannin da ke zargin manyan makarantu fiye da 51 da ke datse kuɗaɗen. An dai yi zargin cewa manyan makarantun na datse kuɗin da ya kai naira 3,500 zuwa naira 30,000 daga kuɗin bashin kowane ɗalibi. Binciken farko-farko ya bayyana yadda aka samu giɓi a rabon kuɗaɗen, inda daga cikin naira biliyan 100 da gwamnatin tarayya ta saki ga tsarin bayar da bashin na NELFUND, naira biliyan 28.8 ne kacal suka isa ga ɗaliban, inda kuma aka nemi naira biliyan 71.2 aka rasa.
Tinubu zai je Katsina ziyarar aiki ta kwana biyu

Tinubu zai je Katsina ziyarar aiki ta kwana biyu

Duk Labarai
Shugaban Najeriya, Bola Tinubu zai kai ziyarar aiki ta kwana biyu zuwa jihar Katsina da ke arewa maso yammacin ƙasar. Cikin wata sanarwa da kakakin shugaban ƙasar, Bayo Onanuga ya fitar, ya ce a ziyarar - wadda zai fara ranar Juma'a - shugaban zai gana da masu ruwa da tsaki domin nazartar yanayin tsaro a jihar. Sanarwar ta ce shugaban zai ƙaddamar da cibiyar ayyukan noma ta zamani da wani titi mai hannu biyu, mai tsawo kilomita 24 da gwamnan jihar, Dikko Radda ya kammala. Haka kuma Bayo Onanuga ya ce Shugaba Tinubu zai kuma halarci ɗaurin auren ƴargidan gwamnan Katsinan kafin kammala ziyarar tasa a jihar.