Sunday, April 19
Shadow
Na rasa wace irin matace Sanata Natasha Akpoti, ta kawo mana korafi, ba’a gama bincike ba ta tsallaka ta kai kara kotu, ba’a gama shari’a ba ta sake tsallakewa ta kai korafi majalisar Dinkin Duniya>>Sanata Godswill Akpabio

Na rasa wace irin matace Sanata Natasha Akpoti, ta kawo mana korafi, ba’a gama bincike ba ta tsallaka ta kai kara kotu, ba’a gama shari’a ba ta sake tsallakewa ta kai korafi majalisar Dinkin Duniya>>Sanata Godswill Akpabio

Duk Labarai
Kakakin majalisar dattijai, Sanata Godswill Akpabio ya koka da irin halayyar Sanata Natasha Akpoti inda yace bai san wane irin tunani gareta ba. Sanata Godswill Akpabio yace ta kawowa kwamitin da'a na majalisar dattijai korafi, ba'a gama bincike ba ta tafi ta kai kara kotu, can ma ba'a gama shari'a ba ta tafi ta kai korafi majalisar Dinkin Duniya. Sanata Godswill Akpabio yace irin wannan abun ne zai iya sawa a daina baiwa mata mukaman siyasa.
Bamu yadda da dawowar El-Rufai Jam’iyyar mu ba, yazo ne kawai ya cimma burinsa>>Kungiyar Matasan Jam’iyyar SDP

Bamu yadda da dawowar El-Rufai Jam’iyyar mu ba, yazo ne kawai ya cimma burinsa>>Kungiyar Matasan Jam’iyyar SDP

Duk Labarai
Kungiyar matasan Jam'iyyar SDP sun bayyana cewa basu yadda da komawar tsohon gwamnan Kaduna, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai Jam'iyyar ba. Kungiyar ta bakin shugabanta, Abdulsamad Bello ta bayyana cewa, El-Rufai kawai yana son samun damar da zai cimma burinsa ne a Jam'iyyar. Sun kara da cewa, abin takaici ne yanda Jam'iyyar ta baiwa El-Rufai dama aka tarbeshi hannu biyu-biyu ba tare da la'akarin hadarin da ke tattare dashi ba. Matasan sun ce karamin misali shine yanda El-Rufai da ga zuwansa gashi yana son yayi kaka gida a Jam'iyyar har yayi yunkurin tsike sakataren Jam'iyyar, Dr. Olu Agunloye daga mukaminsa. Kungiyar tace zata yaki duk wani yunkuri na neman mikawa El-Rufai Jam'iyyar inda suka gargadi shuwagabannin Jam'iyyar kada su aikata haka.
Salah ya lashe kyautar gwarzon ɗan wasan Premier na wata karo bakwai a tarihi

Salah ya lashe kyautar gwarzon ɗan wasan Premier na wata karo bakwai a tarihi

Duk Labarai
Ɗan wasan Liverpool, Mohamed Salah ya lashe kyautar gwarzon ɗan wasan gasar Premier na wata-wata karo na bakwai a tarihin. Mohamed Salah ya lashe kyautar watan Fabrairu a matsayin ɗan wasan da ya fi hazaƙa a watan, bayan da bajintar da ya yi a watan, a ƙoƙarin da ƙungiyarsa ke yi na lashe gasar Premier. Ɗan wasan na ƙasar Masar ya ci ƙwallo shida, ciki har da biyu da ya zura a ragar Bournmouth da wanda ya zura a ragar Manchester City a watan, sannan ya taimaka aka ci huɗu. Mo Salah ya samu kyautar ne bayan doke Beto da Jean-Philippe Mateta da Yankuba da Djed Spence da kuma Dominik Szoboszlai. Da wannan nasara, a yanzu Salah ya kamo tarihin da Sergio Aguero da Harry Kane suka kafa na cin kyautar sau bakwai. Sannan ya zarta Steven Gerrard da Cristiano Ronaldo waɗanda suka ci k...
Wata mata ta kkàshè kishiyarta a jihar Jigawa

Wata mata ta kkàshè kishiyarta a jihar Jigawa

Duk Labarai
Hukumomin ƴansanda a jihar Jigawa da ke arewa maso yammacin Najeriya sun cafke wata mata bisa zarginta da kashe kishiyarta ta hanyar zuba mata ruwan zafi. Lamarin ya faru ne a ƙauyen Buju da ke ƙaramar hukumar Dutse babban birnin jihar Jigawa, kuma bayanai na cewa matar ta rasa ranta ne sakamakon rashin jituwar da ta kaure tsakaninta da abokiyar zamanta. Kakakin rundunar ƴansandan jihar, SP Lawan Shi’isu Adam ya shaida wa BBC cewa matar ‘yar shekara 20 ta watsa wa abokiyar zamanta tafasasshen ruwan zafi ne, sakamakon taƙaddamar da ta kaure tsakaninsu. SP Shi’isu Adam ya ce marigayiyar ta samu mummunan ƙuna, inda aka kai ta asibiti daga baya kuma ta rasu a can. Mai unguwar ƙauyen, Malam Kabiru Abbas ya shaida wa BBC cewa bayan ƙura ta lafa, wadda aka watsa wa ruwan zafin, kafin ...
El-Rufai ya bude shafin TikTok, ya samu mabiya 200,000 cikin Awa 24

El-Rufai ya bude shafin TikTok, ya samu mabiya 200,000 cikin Awa 24

Duk Labarai
Tsohon Gwamnan Jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, ya bude shafi a dandalin sada zumunta na TikTok. Cikin awa 24 kacal da budewa, El-Rufai ya samu sama da mabiya 200,000, yayin da bidiyon sanarwarsa ya tara masu kallo miliyan 1.9 da kuma sharhi (Comment )sama da 21,000. A cikin bidiyon, El-Rufai ya bayyana cewa shafinsa na TikTok zai mayar da hankali kan ra’ayoyinsa a siyasa da kuma sabuwar jam’iyyarsa, SDP. "Wannan shine kawai shafina na gaskiya a TikTok. Ku biyo ni domin kallon bidiyo, yin sharhi da tattaunawa kan siyasar Najeriya da ayyukan sabuwar jam’iyyarmu, SDP. Maraba da ku," in ji shi.
Da Ban cire tallafin man fetur da daukar matakai masu tsauri ba da Najeriya ta talauce saboda shuwagabannin da suka gabata wadaka suka yi da dukiyar daya kamata a gina Al’umma>>Tinubu

Da Ban cire tallafin man fetur da daukar matakai masu tsauri ba da Najeriya ta talauce saboda shuwagabannin da suka gabata wadaka suka yi da dukiyar daya kamata a gina Al’umma>>Tinubu

Duk Labarai
Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya bayyana cewada bai cire tallafin man fetur ba da daukar tsauraran matakai na gyaran tattalin arzikin ba da Najeriya ta talauce. Yace amma matakan da ya dauka hadi da goyon baya da hakurin da 'yan Najeriya suka yi masa yasa a yanzu gashi an fara cin amfanin abin. Yace Farashin kayan abinci ya sauka musamman a cikin watan Ramadana sannan kuma gashi Darajar Naira na ta farfadowa a hankali. Shugaban ya bayyana hakane a yayin da ya karbi bakuncin 'yan majalisa da suka yi aiki tare a lokacin yana dan majalisa. Ya kuma bayyana tsarin Dimokradiyya a matsayin tsari mafi kyawu wanda shine yake kawowa kasa ci gaba.
Mata tasa ‘yansanda sun kama mijinta saboda ya kara aure

Mata tasa ‘yansanda sun kama mijinta saboda ya kara aure

Duk Labarai
Wata mata a jihar Legas tasa 'yansanda sun kama mijinta aun kulle bayan da ya kara aure. Mutumin me suna Charles Chiawa an tsareshi a ofishin 'yansanda kamar yanda matarsa, Uche Chiawa ta bukata. Sun shafe shekaru 20 da yin aure inda Charles yace sun fara samun matsala ne bayan da ya kara aure har ya haihu da amaryarsa. Yace yana da damar kara aure saboda auren gargajiya aka musu shi da uwar gidansa. Saidai matar tasa Uche tace ba auren gargajiya kadai suka yi ba, hadda na kotu kuma tace yana yawan dukanta ne shiyasa tasa a tsareshi. Rahoton yace uwargidan mutumin na da alaka da wata DPO na 'yansanda wanda hakanne ya bata damar sawa a daureshi. Amaryarsa ta je ofishin 'yansandan inda ta nemi a sakeshi amma aka ki bata belinsa aka koreta. Saidai da aka nemi jin ta baki...
Ji yanda Wani mutum ya yanke jiki ya fadi ya mùtù a akin karuwa bayan ya kammala abinda yake yana shirin ficewa daga dakin

Ji yanda Wani mutum ya yanke jiki ya fadi ya mùtù a akin karuwa bayan ya kammala abinda yake yana shirin ficewa daga dakin

Duk Labarai
Wani mutum dan kimanin shekaru 31 ya yanke jiki ya fadi ya mutu a dakin karuwa bayan ya kammala abinda yake yana shirin fita daga dakin. Lamarin ya farune a sabuwar Kutunku dake Gwagwalada a baban birnin tarayya, Abuja. Lamarin ya farune ran Asabar da misalin karfe 5 na yamma inda karuwar data ga haka ya ruga ta sanar da manajansu. Manajan ya garzaya dakin inda ya gane mutumin me suna Ajayi Nicholas inda ya yi gaggawar sanar da 'yan uwansa dake yankin. An garzaya dashi Asibiti inda acan likitoci suka tabbatar da ya mutu 'Yansanda sun je wajan inda suka gudanar da bincike kuma tuni aka kai gawar wanda ya mutun makwanci.