Sunday, December 21
Shadow
Akwai yiyuwar Shugaba Tinubu zai yiwa majalisar Zartarwarsa garambawul inda za’a yiwa wasu ministoci canji, za’a kara kirkiro da wasu

Akwai yiyuwar Shugaba Tinubu zai yiwa majalisar Zartarwarsa garambawul inda za’a yiwa wasu ministoci canji, za’a kara kirkiro da wasu

labaran tinubu ayau, Siyasa
Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya kammala shiri tsaf dan yiwa majalisar zartarwarsa garambawul inda za'a kirkiro karin wasu ministoci da ma'aikatu. Daily Trust tace daga cikin sabbin ma'aikatun da ake son kirkirowa akwai ta kula da dabbobi wadda za'a cire daga ma'aikatar noma. Wannan ma'aikatar ana tunanin zata kawo mafita ga rikicin manoma da makiyaya dake faruwa duk shekara. Hakanan bayan kirkirar sabbin ma'aikatu ana kuma tunanin shugaban kasan zai samar da kananan ministoci a sauran ma'aikatun da basu dasu. Masu kula da al'amuran yau da kullun da masu sharhi a harkokin siyasa sun caccaki gwamnatin Tinubu saboda kin saka kananan ministoci a wasu ma'aikatu
Ba A Bi Umarnin Da Tsohon Shugaban Kasa Muhammadu Buhari Ya Bayar Na Sake Fasalin Naira Ba>>Tsohon Daraktan CBN Ga Kotu

Ba A Bi Umarnin Da Tsohon Shugaban Kasa Muhammadu Buhari Ya Bayar Na Sake Fasalin Naira Ba>>Tsohon Daraktan CBN Ga Kotu

labaran tinubu ayau, Siyasa
Tsohon Daraktan Ayyuka na Kudi a Babban Bankin Najeriya (CBN), Ahmed Bello Umar, ya shaida wa babbar kotun Abuja da ke Maitama cewa ba a bi umarnin da tsohon shugaban kasa Muhammadu Buhari ya bayar na sake fasalin Naira ba. Ya bayyana cewa takardar kudin Naira da aka sake gyarawa a karkashin tsohon Gwamna Godwin Emefiele sun sha bamban da bayanan da tsohon shugaban kasar ya amince da su. Daga: Abbas Yakubu Yaura
Da Dumi-Dumi: ‘Nan Ba da Jimawa Ba Za Mu Aikawa Majalisa Da Kudirin Doka Kan Sabon Albashin Ma’aikata’ – Tinubu

Da Dumi-Dumi: ‘Nan Ba da Jimawa Ba Za Mu Aikawa Majalisa Da Kudirin Doka Kan Sabon Albashin Ma’aikata’ – Tinubu

labaran tinubu ayau, Siyasa
Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya ce nan ba da dadewa ba zai aika da sabuwar dokar mafi karancin albashi ga majalisar dokokin kasar Tinubu ya bayyana hakan ne a jawabinsa na ranar dimokradiyya a ranar Laraba. Ya ce gwamnatinsa ba ta murkushe kungiyar kwadago ba kamar yadda gwamnatin kama-karya ta yi. “Mun yi shawarwari cikin nasara kuma mun yi tattaunawa tare da kungiyoyin kwadago a kan mafi karancin albashi na kasa, nan ba da jimawa ba za mu aika da kudirin zartarwa ga Majalisar Dokoki ta kasa domin tabbatar da abin da aka amince da shi a cikin shekaru biyar masu zuwa ko kasa da haka,” in ji shi. Ku tuna cewa kwamitin mafi karancin albashi na kasa ya mika rahotonsa ga shugaban kasa a ranar Litinin. A cikin rahoton, gwamnatin tarayya ta gabatar da shawarar mafi karancin alb...
Akwai barazanar ambaliya a jihohi 31 da ƙananan hukumomi 148′

Akwai barazanar ambaliya a jihohi 31 da ƙananan hukumomi 148′

Siyasa
Hukumar Bayar da agajin gaggawa ta Najeriya, NEMA ta ce akwai hasashen jihohin ƙasar 31 da ƙananan hukumomi 148 ka iya fuskantar ambaliya a damunar bana. Hukumar ta buƙaci gwamnatocin jihohin ƙasar da su bi gargaɗinta sannan su aiwatar da matakan kariya daga bala'in ambaliya domin tabbatar da kare rayuka da dukiyoyi al'umma. Shugabar hukumar, Zubaida Umar wadda ta tabbatar da hakan a yayin wata ganawa da jami'an gwamnatin jihar Edo, ta nanata muhimmancin haɗa ƙarfi da ƙarfe da jihar wajen samar da shirin ko-ta-kwana domin tunkarar barazanar ta ambaliya. Hukumar ta NEMA dai ba ta lissafa jerin sunayen jihohin da ƙananan hukumomi ba amma ta ce yawanci birane da garuruwan da ke kusa da ruwa ka iya fuskantar barazanar.
Tinubu bai faɗi nawa albashi mafi ƙanƙanta zai kasance ba a jawabinsa

Tinubu bai faɗi nawa albashi mafi ƙanƙanta zai kasance ba a jawabinsa

labaran tinubu ayau, Siyasa
Shugaba Tinubu ya ce gwamnatinsa za ta aike da ƙudiri ga Majalisar Dokokin ƙasar wanda zai kunshi adadin abin da aka amince da shi ya zama albashi mafi ƙanƙanta ga ma'aikata a "matsayin wani ɓangare na "dokokinmu" a shekaru biyar ko ƙasa da haka masu zuwa. Shugaban wanda ya faɗi hakan ne a yayin jawabinsa ga ƴan Najeriya albarkacin ranar dimukraɗiyya, ya ce lallai yana sane da halin matsin tattalin arzikin da 'yan najeriyar ke ciki. To sai dai ya nemi "yan ƙasar da su tallafa wajen cimma "dimukraɗiyyar da za ta tabbatar da cigaban tattalin arziki." Ƴan Najeriya dai sun yi fatan jin ƙarin albashin da suka samu daga bakin shugaban nasu a jawabin nasa na safiyar Talata. A ranar Litinin ne dai kwamitin mutum 37 da aka kafa kan albashin mafi ƙanƙanta ya miƙa rahotonsa bayan kwashe kima...
Da ɗumi-ɗumi: Ana sarai Erik ten Hag zai sanya sabon kwantaragi a Manchester United nan bada jimawa ba

Da ɗumi-ɗumi: Ana sarai Erik ten Hag zai sanya sabon kwantaragi a Manchester United nan bada jimawa ba

Kwallon Kafa
Da ɗumi-ɗumi: Ana sarai Erik ten Hag zai sanya sabon kwantaragi a Manchester United nan bada jimawa ba. Bayan hukuncin INEOS na cigaba da ajiye ten Hag a matsayin mai horas da United, Yanzu shirin ƙungiyar shine ayi gaggawar fara tattauna sabuwar yarjejeniyar tsawaita zaman sa. Manchester United na son nuna amincewar ta gaba ɗaya akan mai horaswar hakanne yasa zata bashi damar ƙara tsawaita zama a Old Trafford domin a cigaba tafiyar tare. Tattaunawa tayi nisa, kaɗan ya rage komai ya kammala! Fagen Wasanni

Yadda ake amfani da tsinken gwajin ciki

Gwajin Ciki
Tsinken Gwajin ciki na bayar da sakamako me kyau idan aka yi amfani dashi yanda ya kamata. Saidai kamin a yi amfani dashi, masana sun ce ya kamata a bari sai bayan kwnaki 10 banyan yin jima'i, ko kuma idan ana son sakamako wanda yafi kyau a bari sai bayan kwanaki 14, wasu ma sun ce kamata yayi a bari sai bayan kwanaki 21 da yin jima'i yayin da wasu suka ce a bari sai idan ba'a ga jinin al'ada ba. Shawara anan itace, idan kin kagara ki ga sakamakon kina iya yin gwajin a duka lokutan guda 3 ko hudu, watau ki yi bayan kwanaki 10 da bayan kwanaki 14 da bayan kwanaki 21 da kuma bayan baki ga jinin al'ada ba. Yanda ake amfani da tsinken gwajin ciki shine, Ana samin kofi ko mazubi sai a yi fitsari a ciki, sai a saka rabin tsinken a cikin fitsarin. Sai ki fiddoshi ki ajiyeshi a kwance ...

Yadda ake gwajin ciki da fitsari

Gwajin Ciki
Gwajin ciki da fitsari shine mafi bada sakamako me kyau. Idan dai an yi gwajin bayan kwanaki 10 zuwa 14 da yin jima'i to lallai za'a ga sakamako me kyau sosai. Akwai hanyoyi da yawa da ake amfani dasu wajan gwajin ciki da fitsari amma wanda suka fi shahara kuma likitoci suka fi yadda dashi shine na tsinken gwajin ciki da ake sayarwa a kyamis. Ana samun mazubi ne ko kofi sai a yi fitsarin a ciki si a saka Rabin tsinken gwajin cikin a ciki, sai ki yi kamar kina kirge da yatsunki, ki kirga 7 ko 10, shikenan sai a cire, a ajiye shi a kwance. Yawanci za'a iya ganin sakamakon gwajin cikin minti 1 ko zuwa 5. Idan tsinken ya nuna layi biyu to kina da ciki amma idan ya nuna layi daya, baki da ciki. Masana sunce zai fi kyau a bari sai an yi batan wata kamin a yi duk wani gwajin dau...
Bayan haihuwar ‘ya’ya 2, Tauraron mawakin Najeriya, Davido da budurwarsa, Chioma zasu je a daura musu aure a Legas

Bayan haihuwar ‘ya’ya 2, Tauraron mawakin Najeriya, Davido da budurwarsa, Chioma zasu je a daura musu aure a Legas

Nishadi
Bayan kwashe shekaru suna soyayya hadda samun 'ya'ya 2, karshe Tauraron mawakin Najeriya, Davido da budurwarsa Chioma zasu je a daura musu aure a Legas. Zadai a musu daurin auren gargajiyane da ake cewa Traditional Wedding. Kuma za'a daura aurenne ranar 25 ga watan Yuni, kamar yanda wasu majiyoyi auka ruwaito. Shima dai Davido da kansa ya tabbatar da hakan.
Fasarar Jawabim Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu Na Murnar Cikar Nijeriya Shekaru 25 A Mulkin Dimokradiyya

Fasarar Jawabim Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu Na Murnar Cikar Nijeriya Shekaru 25 A Mulkin Dimokradiyya

labaran tinubu ayau, Siyasa
RANAR DEMOKARADIYA.12/JUNE/2024. Ya ku yan uwanayan Najeriya bari mu fara da taya juna murnar sake ganin zagayowar ranar Demokaradiya a yau, ranar sha biyu ga watan Yunin shekara ta dubu biyu da ashirin da hudu. Wannan ranar ta zo dai dai da cikar kasar mu shekaru Ashirin da biyar a cikin mulkin Demokaradiya ba tare da katsewa ba. A rana irin ta yau, shekaru talatin da daya baya, muka kaddamar da kudirin mu na zamowa al`ummar da ta yi cikakkiyar amincewa da Demokaradiya. Ba abu ne mai sauki ba, kusan ma cike yake da hadarin gaske ta inda cikin shekaru shida da suka biyo baya sai da duk muka rikide muka zamoyan gwagwarmayar kwatan yancin kanmu a matsayin mu nayan kasa kuma halittun Allah a ban kasa. A cikin wannan gwagwarmayar, mun rasa rayukan gwaraza maza da mata. Ciki kuwa ha...