Thursday, January 22
Shadow
Kasashen Larabawa sun sha Alwashin ba zasu bar Falas-dinawa su sake mallakar makamai ba bayan yakin su da Israela

Kasashen Larabawa sun sha Alwashin ba zasu bar Falas-dinawa su sake mallakar makamai ba bayan yakin su da Israela

Labaran Falasdinawa, Labarin Yakin Gaza, Yakin gaza da isra'ila
Rahotanni sun bayyana cewa, kasashen Larabawa sun dauko alwashin ba zasu sake barin Falas-dinawa au mallaki makamai ba bayan an gama yaki tsakaninsu da Israela. Hakan na zuwa ne yayin da ake tsammanin za'a cimma yarjejeniyar tsagaita wuta tsakanin Israela da Kungiyar Hamas. Saidai abin tambaya anan shine, anya kasashen Larabawan zasu iya aikata hana Falas-dinawa mallakar makamai? Dalili kuwa shine a yanzu gashi ana ta kashesu babu kasar Larabawan data shigar musu ko ta tsaya musu, an zura ido ana kallo Israela na musu kisan kare dangi, ta yaya zasu yadda a hanasu mallakar makamai bayan sun san duk randa Israela ta sake far musu da yaki babu me tare musu? Wannan dai abune me kamar wuya.
Hotuna:Cristiano Ronaldo ya kare kakar wasan bana ba tare da kofi ba inda Al Hilal ta doke kungiyarsa ta Al Nassr, Kalli Hotuna da Bidiyonsa yana kuka, Magoya baya suna tsokanarsa ta hanyar kiran sunan Messi

Hotuna:Cristiano Ronaldo ya kare kakar wasan bana ba tare da kofi ba inda Al Hilal ta doke kungiyarsa ta Al Nassr, Kalli Hotuna da Bidiyonsa yana kuka, Magoya baya suna tsokanarsa ta hanyar kiran sunan Messi

Kwallon Kafa, Labaran Cristiano Ronaldo
Kungiyar Al Hilal ta lashe kofin King Cup na Saudi Pro League bayan doke Al Nassr da ci 5-4 a bugun daga kai sai me tsaron gida. Wannan ne kofi na biyu da kungiyar ta lashe a shekaru biyu a jere. Abin bai yiwa Cristiano Ronaldo dadi ba a wasan da aka buga jiya Juma'a a filin wasa na King Abdallah. An kammala wasan Cristiano Ronaldo yana kuka inda abokan wasansa suka rika bashi baki. https://twitter.com/centregoals/status/1796654446396797079?t=IljN_zZoTlKOgbxoo5HmzA&s=19 Da yawa dai sun ce basu taba ganin Ronaldon a cikin irin wannan halin ba. https://twitter.com/WeAreMessi/status/1796788372368699805?t=A6iDAswCtRpc0vRS7MyxFQ&s=19 A yayin da yazo fita daga Filin, magoya bayan Al Hilal sun rika kiran sunan Messi dan su bashi haushi. A karin farko a tari...
Biden ya yi kira ga Isra’ila da Hamas su amince da sabuwar yarjejeniyar tsagaita wuta

Biden ya yi kira ga Isra’ila da Hamas su amince da sabuwar yarjejeniyar tsagaita wuta

Labaran Falasdinawa, Labarin Yakin Gaza, Yakin gaza da isra'ila
Shugaba Biden na Amurka ya yi kira ga Isra'ila da Hamas su amince da sabuwar yarjejeniyar tsagaita a yakin da suke yi tsakaninsu. Yarjejeniyar za ta sa jami'an Isra'ila su tsagaita wuta ta tsawon mako shida, sannan Hamas ta saki Isra'ilawan da ta yi garkuwa da su - a kuma saki Falasdinawan da ake tsare da su a gidajen yari a Isra'ila. Yarjejeniyar ta yi tanadin Isra'ila za ta janye daga yankunan Gaza sannan ta kyale a rika shiga da kayayyakin agaji. Yayin da za a a ci gaba da tattaunawa, yarjejeniyar za ta ci gaba da aiki har a kai ga sakin duka wadanda aka yi garkuwa da su. Daga nan dakarun Isra'ila su fice daga Gaza Falasdinawa su koma gidajensu su ci gaba da rayuwa.
ALLAH SARKI: Ga Damina Ta Zo Amma Kauyyka Da Dama A Jihar Sokoto Sun Zama Kufai Babu Halin Noma Saboda Matsalar Tsaro

ALLAH SARKI: Ga Damina Ta Zo Amma Kauyyka Da Dama A Jihar Sokoto Sun Zama Kufai Babu Halin Noma Saboda Matsalar Tsaro

Sokoto
ALLAH SARKI: Ga Damina Ta Zo Amma Kauyyka Da Dama A Jihar Sokoto Sun Zama Kufai Babu Halin Noma Saboda Matsalar Tsaro Tun daga1-Tashar Bagaruwa,2-Gidan Auta,3-Teke mai kasuwa,4-Tashar Ango,5- Teke mai Fuloti,6- Gidan Alewa,7- Kuka Majema,8- Kuka Tudu,9-Kuka,10-Inwala,11-Gidan Ayya,12- Santar Dan Hillo,13- Hawan Diram,14- Dakwaro, duk sun watse ba mutane, gashi ruwan shuka sun sauka amma an kori jama'a daga gidajen su maimakon suyi shukar da za su noma, wannan tashin hankalin dame ya yi kama? Muna kira ga hukumomin da wannan al'amarin ya shafa da suyi gaugawar ɗaukar matakan da suka dace. Ya Allah albarkacin wannan ranar ta Juma'a ka kawo mana karshen wannan tashin hankalin. Daga Rabiu Abdullahi KG31/5/202423/11/1445
Tsananin zafi na ci gaba da kashe mutane a Indiya

Tsananin zafi na ci gaba da kashe mutane a Indiya

Duk Labarai
Rahotanni na cewa an samu mutuwar mutane da dama sakamakon tsananin zafi a Indiya. Hukumomin jihohin gabashin ƙasar, Odisha da Bihar sun ce mutane 15 ne suka rasu a ranar Alhamis, kuma suna ci gaba da bincike kan lamarin. An haramtawa ma'aikata zirga-zirga a tsakiyar rana. Ana hasashen cewa za a ci gaba da fuskantar tsananin zafi a gabashi yayin da ake hasashen za a samu sauƙin zafin a Arewa maso Yamma da kuma tsakiyar Indiya.
Ƙungiyoyin TUC da NLC za su tsunduma yajin aiki ranar Litinin

Ƙungiyoyin TUC da NLC za su tsunduma yajin aiki ranar Litinin

Siyasa
Gamayyar ƙungiyoyin ƙwadago na TUC da NLC a Najeriya sun yanke shawarar tsunduma yajin aikin sai baba ta gani sakamakon rashin cimma yarjejeniya tsakaninsu da gwamnatin tarayya. Gamayyar ƙungiyoyin sun sanar da hakan ne da yammacin ranar Juma'a bayan wani taro da suka yi inda suka tattaunawa yiwuwar tsunduma yajin aikin. A farkon makon nan ne dai manyan ƙungiyoyin ƙwadago guda biyu suka yi watsi da tayin naira 60 da gwamnatin tarayya ta yi masu a matsayin albashi mafi ƙanƙanta, biyo bayan zaman da suka yi da gwamnatin tarayya, inda a nan ne gwamnatin ta yi tayin. Da farko dai sai da gwamnatin Najeriyar ta fara kara naira dubu uku a kan tayin naira dubu 47 da ta yi a baya. Su ma ƙungiyoyin ƙwadagon sun rage dubu uku daga naira 497 da suke nema a matsayin albashi mafi ƙanƙanta....
‘Matsalar Najeriya sai a ce ka cancanta amma ba ka da kuɗi’

‘Matsalar Najeriya sai a ce ka cancanta amma ba ka da kuɗi’

Kano, Rabiu Musa Kwankwaso, Siyasa
Ɗan takarar shugaban Nijeriya na jam'iyyar NNPP a zaɓen 2023, ya zargi 'yan ƙasar a kan fifita siyasar kuɗi maimaikon zaɓar mutane masu aƙidar da za su iya kawo canji. Injiniya Rabi'u Musa Kwankwaso ya ce dimokraɗiyyar Najeriya ta samu koma-baya saboda wasu 'yan siyasa da kan sayi ƙuri'un mutane ta hanyar ba su atamfa ko taliya. A cewarsa, irin wannan tunani na ɗaya daga cikin abubuwan da suka jefa al'ummar ƙasar cikin halin matsin rayuwa da taɓarɓarewar tsaron da hukumomi suka gaza shawo kansu ya zuwa yanzu. Ya kuma ce rashin iya mulki ne ya haddasa taɓarɓarewar al'amura kamar tsaro da tattalin arziƙi a Najeriya. Rabi'u Musa Kwankwaso ya bayyana haka a jerin hirarrakin da BBC ta yi da wasu ƙusoshin siyasar Nijeriya a wani ɓangare na cika shekara 25 da mulkin dimokraɗiyya karon...
Bidiyo: Ya Allah ka Bani Yarinya me Hali da Dabi’u irin na Murja Kunya>>G Fresh Al’amin

Bidiyo: Ya Allah ka Bani Yarinya me Hali da Dabi’u irin na Murja Kunya>>G Fresh Al’amin

G-Fresh Al'amin, Murja Ibrahim Kunya, Nishadi
Tauraron dan Tiktok kuma mawaki, G-Fresh Al'amin yayi rokon Allah ya bashi diya kamar Murja Kunya. An ganshi a wani Bidiyo ya daga hannuwa sama yana rokon Allah ya bashi diya irin Murja. G-Fresh ya kuma yi fatan cewa duk abinda yake yi, yana son dansa shima yayi. Kalli Bidiyon anan: https://www.tiktok.com/@kanostatematerial/video/7375257438032874757?_t=8mpTddptPJl&_r=1 G-Fresh dai na daya daga cikin mutanen da suka fi daukar hankula a shafin na Tiktok shi da murja Kunya. Da yawa dai na Allah wadai da abinda Murja Kunya ke yi a shafin na Tiktok inda kwanannan sai da aka kamata har aka kaita Asibitin Mahaukata a Kano. Saidai daga baya ta bar Kano inda tace ita da garin har Abada.
Hotuna:Hadiza Gabon ta bayyana ainahin shekarunta yayin da take murnar zagayowar ranar haihuwarta

Hotuna:Hadiza Gabon ta bayyana ainahin shekarunta yayin da take murnar zagayowar ranar haihuwarta

Hadiza Gabon, Kannywood
Tauraruwar Fina-finan Hausa, Hadiza Gabon ta yi murnar zagayowar ranar haihuwarta inda tace ta cika shekaru 35. Hadiza ta bayyana hakane a shafinta na sada zumunta inda kuma masoya da abokan arziki suka yi ta tayata murna. Da yawa dai masu murnar ranar haihuwarsu basu cika bayyana shekarunsu ba, amma Hadiza Gabon ta yi ta maza ta bayyana cewa shekarunta 35. Ko da yake a hakan ma wasu da yawa sukan karyata. Daga cikin abokan aikin Hadiza Gabon: Shamsu Dan iya ya tayata Murna inda ya saka hotonsu tare a shafinsa da yi mata fatan Alheri: Sauran wanda suka taya Hadiza Gabon murna sun hada da Dj Abba, Hassan Giggs, da dai sauransu.