Majalisar Dattijai na tantance manyan hafsoshin sojin Najeriya
Majalisar dattijan Najeriya na aikin tantance manyan hafsoshin sojin ƙasar waɗanda shugaban ƙasar Bola Tinubu ya zaɓo domin jan ragamar ɓangaren tsaro na ƙasar.
Manyan hafsohin sojin sun isa harabar majalisar da misalin ƙarfe 10 zuwa 11 na safe.
Da farko majalisar ta bayyana cewa za ta gudanar da tantancewar ne a mako mai zuwa, sai dai daga baya ta yanke shawarar matso da tantancewar zuwa yau Laraba
Shugaban Majalisar Dattijan Najeriya, a ranar Talata, ya ce akwai buƙatar gaggauta tantance shugabannin tsaron domin ba su damar ci gaba da gudanar da ayyukansu.
A ranar 24 ga watan Oktoba ne Shugaba Tinubu ya gudanar da sauye-sauye a jagorancin ɓangaren tsaro na ƙasar, inda aka sauya hafsan hafson ƙasar Christopher Musa da Laftanar-Janar Olufemi Olatubosun Oluyede.
Haka nan shug...








