
Shugaban hukumar zabe me zaman kanta, Farfesa Joash Amupitan ya bayyana cewa, sai da Allah ya masa wahayi kai tsaye kamin ya karbi shugabancin INEC.
Ya bayyana hakane a yayin da yake jawabi a wata coci a Abuja.
Yace in banda Allah ya bashi tabbacin cewa zai dafa masa kuma zai karfafashi da ba zai karbi shugabancin INEC din ba.
Ya kara da cewa, da karfin Allah yasan zai yi nasara a game da komai da yake.