Thursday, February 5
Shadow

Wannan abin kunya da yawa yake, A samu wasu su sasanta Sanata Natasha da Akpabio>>Inji Kungiyar Kiristoci ta CAN

Kungiyar Kiristocin Najeriya, CAN ta nemi a samu wasu su shiga tsakani kan rikicin dake faruwa tsakanin Sanata Godswill Akpabio da Sanata Natasha Akpoti.

Shugaban kungiyar reshen Arewa da Abuja, Rev. John Joseph Hayab ne ya bayyana haka a wata sanarwa da ya fitar ga manema labarai,.

Yace ‘yan Najeriya na kallon ‘yan majalisar da mutunci kada su bari lamarin ya canja.

Yace kamata yayi a yi kokarin kare mutuncin ‘yan majalisar dama ‘yan Najeriya baki daya.

Karanta Wannan  Sowore ya ki amincewa ya shiga hadakar sabuwar jam'iyyar su El-Rufai da Atiku inda yace basu da banbanci da Tinubu duk taron barayi ne

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *