Saturday, January 10
Shadow

Ya kamata a wayar da kan Mutane: Irin yanda yawan mutane ke karuwa a Najeriya na damuna>>Shugaba Buhari

Shugaban kasa, Muhammadu Buhari ya bayyana cewa, irin yanda yawan mutane ke karuwa a Najeriya lamarin na damunshi.

Ya bayar da shawarar cewa, ya kamata a wayar da kawunan mutane game da hakan.

Shugaban ya bayyana hakane bayan kammala sallar Idi a jiya, Lahadi.

Ya kuma bayyana farin cikinsa kan yanda mutane da yawa suka rungumi harkar Noma.

Shugaban yace nasarar kasa ta dogara ne akan zamun shuwagabanni masu nasara akai-akai.

Karanta Wannan  Tunda ake Najeriya ba'a taba yin shugaban kasa me karfin Gwiwa kamar ni ba, na yi abinda shuwagabannin baya suka ji tsoron yi, watau cire tallafin man fetur ba tare da tunanin sake zabe na ba>>Tinubu

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *