Friday, May 23
Shadow

‘Yan Bindiga sun kashe ‘yansanda 5 da sojoji 2 a Jihar Zamfara

Kwamishinan ‘yansandan jihar Zamfara, Muhammad Shehu Dalinja ya tabbatar da mutuwar ‘yansanda 5 da sojoji 2 wanda ‘yan Bindiga suka kashe a karamar hukumar Tsafe dake jihar.

Ya bayyana cewa ‘yan Bindigar sun yiwa jami’an tsaron kwantan baunane inda suka bude musu wuta a kan hanyar Gusau zuwa Funtua ranar Alhamis.

Ya bayyana cewa, ‘yan Bindigar sun tafi kaiwa kamfanin gini na Setraco Company Hari ne inda jami’an tsaron suka samu bayanan sirri suka tafi dan taresu.

Yace yanda aka yi suka kashe musu jami’ai kenan.

Karanta Wannan  Wata Sabuwa: Iyalan marigayi Shugaban sojojin, Lagbaja sun yi zargin cewa kasheshi aka yi

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *