Friday, December 5
Shadow

‘Yansanda a jihar Katsina sun dakile yunkurin gàrkùwà da mutane inda suka kubutar da mutane 21

Hukumar ‘yansandan Najeriya ta sanar da cewa ta dakile yunkurin garkuwa da mutane a karamar hukumar Jibia dake jihar Katsina inda ta kubutar da mutane 21.

Kakakin ‘yansandan jihar, ASP Abubakar Sadiq-Aliyu ne ya bayyana haka a wata sanarwa da ya fitr ga manema labarai inda yace sun samu wannan nasara ne a aikin da suka yi tare da sojoji da kuma ‘yan Bijilante.

Yace sun dakile yunkurin garkuwa da mutanen ne a Ka’ida, Unguwar One Boy, da Danmarke quarters duka a Jibia ranar 7 ga watan Nuwamba.

Yacw maharan sun kai harinne inda su kuma suka kai dauki cikin gaggawa inda aka shafe awa guda ana bata kashi.

Karanta Wannan  KARON FARKO: Shugaban Ƙasar Amurka, Donald Trump, ya ziyarci Babban Masallacin Sheikh Zayyad da ke Abu Dhabi, wanda ke ɗaya daga cikin manyan masallatai a duniya mai cike da fasahar gini ta zamani

Yace ‘yan Bindigar sun tsere daga wajan ba shiri.

Yace sun kubutar da mutane 16 saidai 5 daga ciki sun samu raunukan bindiga.

Yace jami’in Bijilante daya da jami’in hukumar tsaro mallakin jihar ta Katsina sun samu raunuka.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *