Friday, December 5
Shadow

YANZU-YANZU: Babiana Ta Fitar Da Takardar Saki Ukkun Da Mìjinta Yayi Mata

DAGA Shafin Dokin Karfe TV

Jarumar Tik-Tok Hafsat Waziri, wadda aka fi sani da Babiana ta bayyana cewa mijinta ya sake ta saki uku dan haka, yanzu haka ba ta da aure kuma ta ga cewa bai kamata ta yi ta ɓoye-ɓoyen sakin da mijinta yayi mata ba gara ta fito ta shaidawa Duniya halin da take ciki.

Jaridar Dokin Ƙarfe TV ta samu takardar shaidar sakin wadda Babiana Waziri ta aiko mata inda a ciki aka bayyana cewa “Ni Muhammad Izzudden Eze na saki matata saki uku”. An rubuta takardar ranar 11 ga watan 4 na shekarar 2024, kamar yadda kuke gani.

Karanta Wannan  Sadiya Haruna Ta Grime Ni, Shekaru Na 35 Ita Kuma Shekarunta 48, Kuma Kafin Mu Rabu Na Ba Ta Hakuri Ya Fi Sau Milyan Duk Da Cewa Ita Ta Yi Min Laifi, Saboda Na Kama Ta Tana Cin Abinci Da Wani Gardi Da Muharraminta Ba, Cewar G-Fresh Al'Amin

Babiana ta kuma bayyana cewa “Na shiga bala’in rayuwa a dalilin aurensa da nayi, har asibitin mahaukata an kai ni a dalilin aure kuma har yanzu ban gama farfaɗowa ba”. In ji ta.

Daga nan ta ƙara da cewa “Mijina ba ya biya mun buƙatuna na rayuwa ya bar ni, ni nake yi wa kaina komai. Ba daidai ba ne ka auri mata ba ka da kuɗin ciyar da ita da biya mata buƙatunta ba”. In ji ta.

Ta kuma ta ƙara da cewa “Na godewa Allah da jarrabawa ta ta zo a aure. Ni na yi aure don in raya Sunnar ma’aiki amma abin ya zame mun masifa da bala’i”. A cewarta.

Karanta Wannan  Hotuna Kalli Yanda aka yiwa wata uwar yara 3 Allah wadai saboda shigar banza data nuna jikinta sosai

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *