Thursday, December 4
Shadow

Yanzu-Yanzu: Dangote yace zai daina sayarwa da Najeriya man fetur

Rahotonni sun bayyana cewa, Attajirin dan kasuwa Aliko Dangote zai daina sayarwa da Najeriya man fetur.

Jaridar TheCable ta ruwaito cewa Dangote na son daukar wannan mataki ne biyo bayan kasa cimma matsaya akan ci gaba da cinikin man fetur din da kudin Naira maimakon dalar Amurka.

Saidai majiyar tace matatar man zata ci gaba da fitar da man fetur din zuwa kasashen waje dan kuwa dama daga kasashen wajen take siyo danyan man da take tacewa.

Matatar Dangote na sayarwa da Najeriya man fetur din data tace ne da Naira saboda a kudin Naira take sayen danyen man fetur da take saya daga hannun gwamnati.

Karanta Wannan  Tsohon Gwamnan jihar Kogi, Yahya Bello da EFCC ke bincike kan zargin Satar Naira Biliyan 80 yace shugaba Tinubu ba sai ya je jikar Kogi yakin neman zabe ba, ya ci zaben 2027 a jihar

Saidai wannan yarjejeniyar a yanzu ta kare.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *