Tuesday, February 3
Shadow

Masu garkuwa da mutane sun sace wata mata a Asibitin dake Kano

Masu garkuwa da mutane sun sace wata mata me shekaru 60 da haihuwa a Asibitin mahaukata dake Dawanau, Karamar hukumar Dawakin Tofa Kano.

Matar me suna Talatu Ali an yi garkuwa da itane a yayin da take jiran ganin Likita.

Dan matar da dan uwanta ne suka kai ta Asibitin, saidai a yayin da suma suke jiran layi ya zo kanta taga likita, sai suka nemeta sama da kasa suka rasa.

Lamarin ya farune ranar February 19, 2025 da misalin karfe 8 na safe, saidai ranar February 21 da misalin karfe 7 na safe an kira danginta inda aka tabbatar musu da cewa an yi garkuwa da itane.

Karanta Wannan  Kungiyar malaman kwalejojin Kimiyya da fasaha, ASUP sun baiwa Gwamnatin Tarayya wa'adin akwanaki 21 a biya musu bukatunsu ko su tafi yajin aiki

Hukumar ‘yansandan jihar ta tabbatar da faruwar lamarin.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *