Friday, December 5
Shadow

Attajirin Najeriya, Aliko Dangote ya cika shekaru 68 a yau

A yau ne attajirin dan kasuwa, Aliko Dangote ke cika shekaru 68 da Haihuwa.

An haifi Dangote a ranar April 10, 1957 a garin Kano.

Mahaifiyarsa Mariya Sanusi Dantata jikace a wajen Attajirin dan kasuwa, Alhassan Dantata.

Mahaifinsa, Mohammed Dangote abokin kasuwancin Alhassan Dantata ne.

Dangote yayi karatu a jami’ar Al-Azhar ta birnin Cairo na kasar Egypt.

Bayan nan ne ya fara yiwa kawunsa Abdulkadir Sanusi Dantata aiki inda daga baya ya karbi bashin $3000 yana da shekaru 21 ya fara kasuwanci.

Dangote yace tun yana makarantar Firamare ya fara kasuwanci.

Karanta Wannan  Kotu ta hana tsohon Gwamnan jihar Kogi, Yahya Bello Fasfo dinsa inda yace yana son ya je kasar waje a duba lafiyarsa, Saidai kotun tace bai bayar da hujjar cewa Likitocin Najeriya ba zasu iya magance rashin lafiyar tashi ba

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *