Thursday, February 5
Shadow

Gyare-Gyaren da muka yi akwai wahala, amma suna bada sakamako me kyau>>Inji Gwamnatin Tarayya

Gwamnan babban Bankin Najeriya, Cardoso ya bayyana cewa, Gyare-Gyaren da gwamnatin tarayya ta zo dasu babu sauki amma suna bayar da sakamako me kyau.

Ya bayyana hakane a wajan taron da aka gudanar a birnin Washington DC na kasar Amurka wanda IMF da bankin Duniya suka shirya.

Yace wadannan Gyare-Gyaren sun dora Najeriya a turbar ci gaba kuma a yanzu suna bayar da sakamako me kyau.

Wasu daga cikin Gyare-Gyaren da gwamnatin tarayya ta kawo sune cire tallafin man fetur, cire tallafin dala da sauransu.

Karanta Wannan  Shin wai Har yanzu ana Tantamar wa yafi wani tsakanin Rarara da Sarkin Waka ko yanzu an gano wanda ke kan gaba?

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *