Sunday, March 15
Shadow

Gwamnatin Kano na da kudin da ta fi Karfin Haka: Shehu Sani yace Naira Miliyan daya da Gwamna Abba yace a baiwa kowane iyalan ‘yan kwallon Kano da suka ràsù a hadarin mota ta yi kadan

Tsohon sanatan Kaduna ta tsakiya, Sanata Shehu Sani ya bayyana cewa, Naira Miliyan 1 da Gwamnatin Kano tace a baiwa kowane daga cikin iyala ‘yan Kwallon jihar da suka yi hadari ta yi kadan.

Sanata Sani ya bayyana hakane a shafinsa na sada zumunta inda yace Gwamnatin jihar Kano na da kudin da ya kamata ace abinda zata bayar yafi haka.

Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf da yake aikin hajji, ya ce a baiwa kowane daga cikin iyalan ‘yan kwallon Naira Miliyan 1 sannan a basu kayan abinci kamin ya dawo.

Karanta Wannan  Kalli Bidiyon: An ga Bilal Villa a daji dauke da Bìndyghà, lamarin ya jawo cece-kuce inda ya bayyana cewa sabuwar waka ce

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *