Saturday, May 17
Shadow

Babu Alamar Abubuwa zasu yi sauki a gwamnatin Tinubu>>Inji Archbishop Nwaobia

Wani babban malamin Kiristanci Archbishop Nwaobia ya bayyana cewa babu alamar lamura zasu gyaru a gwamnatin shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu.

A hirar da wakilin jaridar sunnewsonline suka yi dashi, ya bayyana cewa faduwar darajar Naira akan Dalar Amurka matsala ce babba wadda ta jefa ‘yan Najeriya da yawa cikin halin wahala.

Yace kuma gwamnatin Tinubu ta kasa samo hanyar warware wannan matsala.

Ya kara da cewa, Sam Gwamnatin Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu bata da alkibla dan ta kasa dasa tushen ci gaban Najeriya.

Karanta Wannan  Da Duminsa: Majalisar Jihar Kaduna ta bukaci a kama da hukunta tsohon gwamnan jihar, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai saboda zargin lalata kudin jihar har Naira Biliyan 423

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *