Friday, December 5
Shadow

Kalli Bidiyo: Gwamnan Katsina, Dikko Raddah na shan suka bayan da yace Likitocin Najeriya basu da kishi suna fita aiki kasashen waje maimakon su tsaya Najeriya su taimakawa ‘yan uwansu

Gwamnan jihar Katsina, Dikko Raddah ya bayyana rashin jin dadinsa kan yanda likitoci ke tserewa daga Najeriya suna zuwa kasashen waje aiki.

Gwamnan yace abin takaici shine a baya likitoci mata daga Najeriya basa fita kasashen waje yin aiki amma a yanzu likitoci mata daga Arewa suma sun bi sahu.

Yace irin wadancan kasashe mutanensu ragwayene basa iya karatun aikin Likita shiyasa suke zuwa su baiwa likitocin Najeriya Albashi me tsoka dan su daukesu.

Ya zargi Likitocin da rashin kishin al’ummarsu.

Saidai hakan ya jawowa Gwamnan suka inda wasu ke cewa ba’a kula da hakkokin Likitocin ne sannan ba’a biyansu albashi me kyau shiyasa.

Karanta Wannan  Kalli Yadda Aka Yafawa Ka’aba Sabuwar Riga Albarkacin Shiga Sabuwar Shekarar Musulunci Ta 1447 Bayan Hijira

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *