Sunday, March 15
Shadow

Karamin Ministan tsaro, Bello Matawalle zai aurar da ‘ya’yansa 9

Rahotanni sun bayyana cewa, Karamin Ministan tsaro, Bello Matawalle zai aurar da ‘ya’yansa maza da mata su 9.

Katin gayyatar auren ya watsu sosai a kafafen sada zumunta inda aka ga cewa za’a yishi ne ranar 6 ga watan Fabrairu a babban masallacin Juma’a dake Abuja.

Sunayen ‘ya’yan nasa sune kamar haka, Ibrahim, Suraj, Safiya, Maryam, Aisha, Fahad, Muh’d, Nana Firdausi, and Farida.

Kakakin jam’iyyar APC na jihar Zamfara, Yusuf Idris, ya tabbatar da faruwar lamarin.

Karanta Wannan  Gwamnatin Bauchi ta ware Naira miliyan 400 don sayen kwamfuta guda shida ga ofishin Sakataren Gwamnatin Jihar

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *