
Rahotanni daga jihar Kebbi na cewa, an dakatar da wani malamin makaranta a jihar saboda ya fito ya soki rabon shinkafa da masa Sa’i guda da aka bashi.
Malamin a wani Bidiyonsa da ya watsu sosai a kafafen sada zumunta an ganshi yana fadar cewa shi bai gode ba a matsayinsa na malamin makaranta da aka bashi wannan a matsayin tallafi.
Sahara Reporters ta wallafa cewa, an dakatar da malamin saboda wannan Bidiyon.
A wata takardar dakatarwar da Sahara Reporters ta wallafa, anga cewa an dakatar da malmin me suna Abduljalal Usman na tsawon watanni 3 ba tare da Albashi ba.
Takardar dai ta zargeshi da sakaci da aiki.
Amma a zahirin gaskiya da yawa sun ce saboda wancan Bidiyon ne da yayi.