
Wannan baturen ya zargi Gwamnatin shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu da cewa, ta biya mutane a kasar fan £500 dan su fito kan titi su yabawa Gwamnatin Tinubu.
A kwanakin da ya gabata ne dai shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya je kasar Ingila inda ya gana da Gwamnatin kasar akan alakar Najeriya ta kasuwanci da kasar.