
Rahotanni sun bayyana cewa, Hukumar ICPC ta sake kama tsohon Gwamnan Kaduna, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai a yau bayan zaman kotun da aka yi.
Malam Nasiru Ahmad El-Rufai dai ya nemi beli inda kotu ta saka ranar Laraba, 1 ga watan Afrilu dan yanke hukunci.
A baya dai ICPC sun ce sun saki malam Nasiru Ahmad El-Rufai ne saboda tausayi bayan rasuwar mahaifiyarsa inda ya samu halartar jana’izar da aka mata.