
Rahotanni daga fadar shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu sun bayyana cewa, Fadar ta sayi Dutsen guga guda biyu akan Naira Miliyan 10.
Watau kowanne dutsen guga an sayeshi akan Naira Miliyan 5 kenan.
An saiwa ofishin mataimakin shugaban kasa, wannan Dutsen gugar ne, kamar yanda kafar dake saka ido akan yanda ake kashe kudin Gwamnati, Govspend ta ruwaito.
Lamarin dai ya baiwa mutane mamaki.