Friday, April 10
Shadow

Yanda aka shirya munafurcin Tsigeni a matsayin Gwamna da hadin Bakin Mataimakina, Gwarzo, dan ya gajeni>>Inji Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf

Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya bayar da labarin yanda aka shirya munafurcin tsigeshi a matsayin Gwamna tare da hadin gwiwar mataimakinsa da ya sauka, Gwarzo.

Gwamnan yace an shirya tsigeshi ne sai kuma Gwarzo ya maye gurbinsa.

Yace amma sai Allah bai basu nasara ba.

Gwamnan ya bayyana hakane a yayin ganawa da wasu magoya bayansa.

Yace yaji ance mataimakin nasa ya sauka daga mukaminsa amma har yanzu shi bai ga takardar ajiye aikin nasa ba.

Karanta Wannan  Wata Sabuwa: Obasanjo yace Peter Obi yake son ya tsaya takarar shugaban kasa, Kwankwaso ya masa Mataimaki a ADC

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *