Wednesday, April 15
Shadow

Matsalar tsaron Arewa ta kai matsayin Yaqi>>inji Kungiyar Tuntuba ta Arewa

Kungiyar tuntuba ta Arewa, ACF ta bayyana cewa, matsalar tsaron da ake fama da ita ta kai matsayin yaki.

Kungiyar tace tana kira ga Gwamnati data karkatar ta hankalinta da ma dukkan wani abu daya shafi kudi dan ganin an magance wannan matsala.

Kungiyar ta bayyana matsayar tane bayan zaman data yi.

Zaman ya samu halartar Tsohon shugaban sojoji, Janar Tukur Yusuf, Da Tsohon shugaban ‘yansanda, Muhammad Abubakar, da tsohon sakataren majalisar Dinkin Duniya, Tijjani Muhammad-Bande, da tsohon sakataren gwamnatin tarayya, Mahmud Ahmad, da shugaban kungiyar, Bashir Dalhatu.

Sun bayyana cewa matsalar tsaron na jefa musamman yankin Arewa cikin tawayar tattalin arziki da kuma daidaita iyalai da sauransu.

Karanta Wannan  Hukumar 'yansandan Najeriya zata hukunta 'yansanda masu cin zalin Direbobi suna karbar musu kudi a jihohin Inyamurai

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *