Tuesday, May 5
Shadow

Kai Duniya: Ji hanyar da matashinan ya bi ya yaudari yarinyarnan ya biya bukatarsa da ita ya kuma dauki Bidiyon abinda ya faru

CIKAKKEN BAYANI

Matashi da ya tarwatsa rayuwar yarinyar nan sunansa Muhammad Hassan (Bossman) lambar wayansa 08185**7448 dan jihar Kano ne, ban fitar da cikakken nambar wayansa ba da kuma anguwar da yake a Kano saboda dalilai na bincike

Ita kuma yarinyar a jihar Kaduna take, ba zan fadi cikakken sunanta da anguwarsa ba saboda kiyaye mutuncinta da kuma anguwarsu

Bossman ya hadu da yarinyar ta sanadin media, ya fara nemanta da sunan soyayya, ya yaudareta da cewa zai aureta, ya bita Kaduna ya kama Hotel ya fara rabata da budurcinta

Shine mutum na farko da ya fara zina da ita, wannan bidiyo na tsiraci dake yaduwa ya kai shekara guda da yinsa, bayan ya gama |a|ata rayuwar yarinyar sai yace gaskiya shi ba zai iya aurenta ba

Karanta Wannan  Kalli Bidiyon: Yanda aka tarbi Rahama Saidu a filin Jirgi bayan da ta dawo daga Umrah inda ta kai 'yan uwanta

Shikenan ta watsar da shi, ta samu wani zai aureta, da wannan tsinannen da ake kira Bossman yaji labarin zata auri wani, sai ya fara aika mata wannan bidiyo na barazana ta hannun kawarta, cewa idan ta kuskura tace zata auri wani zai watsa bidiyon

A haka dai har wanda ta samu daga baya zata aura ya samu labari, kuma yace ya amince zai aureta a haka matukar bidiyon bai fita ba

Ana haka yanzu saura wata daya a daura mata aure, to da wancan tsinannen yaji labari sai ya saki bidiyon a media don ya hanata aure ya kuma tarwatsa mata rayuwa

Masu ganin laifin yarinyar ku san irin kalaman da zaku fadi kafin Allah Ya jarrabeku, domin ‘ya’yanku da kuka haifa da kannenku mata basu fi karfin tsinannun maza su yaudaresu su bata musu rayuwarsu ba

Karanta Wannan  Manyan Limaman Kiristoci sun yi ruwan Allah wadai ga gwamnatin Tinubu inda suka ce Ya magance matsalar Talauci data tsaro

Muna kan tattaunawa da iyayenta don daukar matakin shari’a akan tsinanne Bossman, sai ya girbi sakamakon abinda ya aikata da taimakon Allah

ABIN TAUSAYI

Chatting da yarinyar nan tayi da kawar mahaifiyarta bayan bidiyon lalatar da wani tsinanne yayi da ita ya bayyana a media akwai alamun fargaba cikin kalamanta

Wannan magana da tayi yana mai kama da wanda yake shirin kashe kansa, na samo inda yarinyar take, na samu tsinannen da ya mata zaluncin nan

Na isar da shawara da nasiha zuwa ga iyayen yarinyar, na farko su kwantar da hankalinsu akan wannan jarrabawa, na biyu su sa ido sosai a kan yarinyar domin wannan chat din da tayi ya nuna alamun zata iya aikata suicide

Karanta Wannan  Kalli Bidiyon: Irin yanda Atiku Abubakar ya je gidan Amaechi ya zauna yana jiransa a falo be fito ba ya dauki hankula

Saurayinta ne, cin amanarta yayi, zuwa jimawa zan baku cikakken bayanin abinda ya faru da matakin da za’a dauka Insha Allah

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *