
Tsohon sakataren Gwamnatin tarayya, Babachir David Lawal ya bayyana cewa ba siyasar kudi yake yi ba.
Ya bayyana hakane a hirar da aka yi dashi a Channels TV inda yace ba gaskiya bane cewar da ake wai Hayatu-Deen ya bashi kudi dan ya taimaka masa ya ci zaben fidda gwani na dan takarar jam’iyyar ADC.
Yace Hayatu-Deen bashi da kudin da zai bashi a yanzu.
Yace idan yana son kudi, waya kawai zai daga ya kira shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu kuma ya tabbatar kamin ya je gida kudin zasu shiga asusunsa.