Wednesday, July 9
Shadow

An yi kiran Gwamnatin tarayya ta kama Rotimi Amaechi saboda kiran da ya yiwa talakawa cewa su daina yadda ‘yan siyasa da basu wuce mutane Dubu 100 ba na sace dukiyar Najeriya

{“remix_data”:[],”remix_entry_point”:”challenges”,”source_tags”:[“local”],”origin”:”unknown”,”total_draw_time”:0,”total_draw_actions”:0,”layers_used”:0,”brushes_used”:0,”photos_added”:0,”total_editor_actions”:{},”tools_used”:{},”is_sticker”:false,”edited_since_last_sticker_save”:false,”containsFTESticker”:false}

Wata kungiya me suna GMI a takaice ta yi kira ga shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu da ya dauki matakai kan tsohon Ministan Sufuri, Rotimi Amaechi kan kalaman da yayi na cewa Talakawa au daina yadda ‘yan siyasa da basu wuce mutane dubu 100 ba na sacw dukiyar Najeriya.

Amaechi yace Mutanen Najeriya miliyan sama da 200 ne dan haka bai kamata su bari ‘yan siyasar da basu wuce mutane dubu 20 zuwa 100 ba suna sace dukiyar kasarnan ba.

Saidai a sanarwar kungiyar ta bakin shugaban ta, Samaila Musa tace wadannan kalamai na Amaechi zasu iya kawo taahin hankali da zuga talakawa.

Karanta Wannan  Ba Allah ne ya zabi Tinubu ba ya zama shugaban Najeriya, da Karfin Tsiya ya kwace mulki>>Inji Fasto Chukwuemeka Odumeje

Kungiyar ta yi kiran kada talakawa musamman matasa su saurari Amaechi inda tace su kaucewa yin amfani da karfi wajan canja gwamnati, su yi amfani da karfin kuri’arsu.

Hakanan ta yi kiran gwamnatin Tarayya ta dauki mataki kan Amaechi.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *