Wednesday, July 9
Shadow

Duk da ni dan Arewa ne, Amma dan kudu nake son a baiwa takarar shugaban kasa a 2027 a jam’iyyar mu ta ADC>>Datti Baba Ahmad

{“remix_data”:[],”remix_entry_point”:”challenges”,”source_tags”:[“local”],”origin”:”unknown”,”total_draw_time”:0,”total_draw_actions”:0,”layers_used”:0,”brushes_used”:0,”photos_added”:0,”total_editor_actions”:{},”tools_used”:{},”is_sticker”:false,”edited_since_last_sticker_save”:false,”containsFTESticker”:false}

Dan takarar mataimakin shugaban kasa a jam’iyyar Labour party a zaben shekarar 2023, Datti Baba Ahmad ya bayyana cewa, dan kudu yake son a baiwa takarar shugaban kasa a zaben shekarar 2027.

Ya bayyana hakane a hirar da aka yi dashi a Arise TV inda yace alkawari ne da ya kamata a ce an cikashi tsakanin mutanen Arewa da kudancin Najeriya.

Yace Tsohon shugaban kasa, Muhammadu Buhari daga Arewa yayi shekara 8 yana mulki hakanan ya kamata a bar kudu itama ta shakara 8 tana mulki kamin mulkin ya dawo Arewa.

Yace zai yi aiki tukuru dan ganin dan kudu ne aka tsayar takarar shugaban kasa a zaben shekarar 2027 a jam’iyyar ADC.

Karanta Wannan  Kalli Bidiyo: Ashe haka ya iya Rubutu? Kyawun Rubutun mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya dauki hankula

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *