Thursday, May 22
Shadow

Author: Auwal Abubakar

Ta tabbata dai Hadaka me karfi tsakanin Atiku da Peter Obi ta kullu, APC ta kadu inda ta yi magana kan lamarin

Ta tabbata dai Hadaka me karfi tsakanin Atiku da Peter Obi ta kullu, APC ta kadu inda ta yi magana kan lamarin

Duk Labarai
Rahotanni na kara bayyana dake tabbatar da alaka me karfi tsakanin Atiku Abubakar da Peter Obi ta kullu. Rahotannin sun ce, duka bangarorin sun saka hannu a wata yarjejeniya da suka akince da ita. A tafiyar dai akwai tsohon gwamnan Kaduna, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai da Tsohon Ministan sufuri, Rotimi Amaechi da sauransu. Hakanan rahoton yace sun kuma amince da komawa jam'iyyar ADC da kuma saka kudi dan gyara jam'iyyar. Saidai duk da El-Rufai shi yana SDP ne, rahoton yace da zarar an kammala shirya komai, za'a sanar da kulla alaka tsakanin SDP da ADC din. A bangaren APC kuwa, sakataren jam'iyyar Ajibola Basiru ya bayyana cewa shugaban kasa Bola Tinubu shine uban hada kan al'umma kuma suna da yakinin shi zai lashe zaben shekarar 2027.
Da Duminsa: An kàshè ma’aikatan ofishin jakadancin Israeyla 2 a babban birnin kasar Amurka, Washington DC

Da Duminsa: An kàshè ma’aikatan ofishin jakadancin Israeyla 2 a babban birnin kasar Amurka, Washington DC

Duk Labarai
Rahotanni daga babban birnin kasar Amurka, Washington DC na cewa an kashe ma'aikatan ofishin jakadancin kasar Israela 2. An bayyana lamarin da cewa Kiyayya ce ga Yahudawa. Wani rahoto yace maharbin yayi ihun cewa a kyale Falasdinawa kamij ya kashe mutanen. Shugaban kasar Amurka, Donald Trump ya bayyana Allah wadai da lamarin inda yace irin wannan lamari bashi da mazauni a kasarsu.
Gidajen Sayar da Man Fetur kusan Dubu biya sun kulle saboda rashin tabbas na farashi da yawaitar rage farashin da Dangote yake

Gidajen Sayar da Man Fetur kusan Dubu biya sun kulle saboda rashin tabbas na farashi da yawaitar rage farashin da Dangote yake

Duk Labarai
Rahotanni sun ce gidajen saye d man fetur akalla 4900 ne suka kulle a fadin kasarnan saboda rashin tabbas na kasuwar man fetur din. 'Yan kasuwar da yawa basa iya sayen tankar mai, inda a yanzu sai ka da an hada kudi na 'yan kasuwa biyu zuwa uku kamin su samu damar sayen tankar man fetur daya wadda a baya cikin sauki mutum daya ke iya sayenta. Daga watan Janairu na shekarar 2025 zuwa Afrilu matatar man fetur ta Dangote ta rage farashin ta sau 6 inda ya fara a Naira 950 har ya sakko zuwa 835. 'Yan kasuwar da basu ma da kudin da za'a yi wannan hadaka dasu dole tasa sun rufe gidajen man fetur din. Bayan zuwan Gwamnatin Bola Ahmad Tinubu, Ta cire tallafin man fetur wanda hakan yasa farashin ya koma hannun 'yan kasuwa.
Hotunan kananan yara da nake gani suna wahala a Gàzà akwai ban tausai, ina kira gareka da a kawo karshen wannan yàkì>>Shugaban Amurka Donald Trump ya sake yiwa Benjamin Netanyahu magana

Hotunan kananan yara da nake gani suna wahala a Gàzà akwai ban tausai, ina kira gareka da a kawo karshen wannan yàkì>>Shugaban Amurka Donald Trump ya sake yiwa Benjamin Netanyahu magana

Duk Labarai
Rahotanni daga fadar shugaban kasar Amurka, White House na cewa, shugaban Amurka, Donald Trump ya sake yin kira ga Firaiministan Israyla Benjamin Netanyahu da a kawo karshen yakin da suke yi da kungiyar Hàmàs. Trump yace ya damu da hotunan da ya gani na yara suna shan wahala a Gaza yace abin akwai ban tausai. Yace a yi sulhu sannan a saki wadanda aka yi garkuwa dasu sannan a kawo karshen yakin. Jaridar Axios ta kasar Amurka tace wasu majiyoyi biyu sun shaida mata hakan daga fadar ta White House.
Daya daga cikin masu laifin da suka tsere daga gidan yari yace a aikawa mahaifiyarsa Ladar Naira Miliyan 5 da aka saka ga duk wanda ya taimaka aka kamasu shi kuma zai koma gidan yarin da kanshi

Daya daga cikin masu laifin da suka tsere daga gidan yari yace a aikawa mahaifiyarsa Ladar Naira Miliyan 5 da aka saka ga duk wanda ya taimaka aka kamasu shi kuma zai koma gidan yarin da kanshi

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa, Gwamnati ta saka ladar Naira Miliyan 5 ga duk wanda ya taimaka aka kama wadanda suka tsere daga gidan yarin Ilesa na jihar Osun. Saidai wani shafi a Twitter wanda yake ikirarin shi daya daga cikin wadanda ake nema ne yace damfarar dala $20 kawai yayi aka kamashi. Yace amma a aikawa Mahaifiyarsa Miliyan 5 din da aka ce an saka akan duk wanda ya taimaka aka kamasu shi kuma zai koma gidan yarin da kansa. https://twitter.com/illxgally/status/1925263845938852073?t=W7WZEzT9q4WDx1QjtJ9pLg&s=19 Saidai wasu na shakkun cewa ba shi bane.
Dangote ya shiga cikin mutane 100 da suka fi bayar da taimako a Duniya inda yake bayar da kyautar Naira Biliyan 50 duk shekara

Dangote ya shiga cikin mutane 100 da suka fi bayar da taimako a Duniya inda yake bayar da kyautar Naira Biliyan 50 duk shekara

Duk Labarai
Jaridar Time ta saka Dangote cikin mutane 100 da suka fi bayar da kyauta a Duniya. Rahoton yace Dangote yana bayar da kyautar Naira Biliyan 50 duk shekara. Dangote dai shine wanda yafi kowane bakar fata Kudi a Duniya sannan shine na daya a Afrika. A baya, Dangote ya rabawa 'yansandan Najeriya kyautar Motocin aiki.
Gwamnati ta saka ladar Naira Miliyan 5 ga duk wanda ya taimaka aka kama masu laifin da suka tsere daga gidan gyara hali su 7, kalli Hotunansu ko kasan wani

Gwamnati ta saka ladar Naira Miliyan 5 ga duk wanda ya taimaka aka kama masu laifin da suka tsere daga gidan gyara hali su 7, kalli Hotunansu ko kasan wani

Duk Labarai
Gwamnatin tarayya ta wallafa hotunan masu laifi da suka tsere daga gidan gyara hali na Ilesa dake jihar Osun. Gwamnatin tace ta saka ladar Naira Miliyan 5 ga duk wanda ya taimaka aka kama su. Da safiyar ranar Talata ne dai masu laifin suka tsere a yayin da ake tsaka da ruwan sama.
Kalli Bidiyon yanda masunta suka kama Katoton maciji a Kaduna me ban tsoro

Kalli Bidiyon yanda masunta suka kama Katoton maciji a Kaduna me ban tsoro

Duk Labarai
Bidiyon yanda wasu masunta da suka je kamun kifi amma suka kama Katon maciji a jihar Kaduna ya dauki hankula. An ce aun ajiye macijinne har kusan tsawon wata daya inda wani ya sayeshi amma ya rika yunkurin tserewa. Abin dai ya bada mamaki: https://twitter.com/Nasir1on1/status/1925204970732745095?t=hVC6JcLoXlxX71V2rZlvdQ&s=19 Da yawa aun yo mamaki da ganin girman Macijin.
Bankin Duniya yace rabin mutanen Najeriya watau mutane sama da Miliyan 100 sun fada Talauci tsamo-tsamo

Bankin Duniya yace rabin mutanen Najeriya watau mutane sama da Miliyan 100 sun fada Talauci tsamo-tsamo

Duk Labarai
Bankin Duniya yace kusan rabin 'yan Najeriya sun fada cikin talauci tsamo-tsamo saboda tsadar rayuwa dake karuwa akasar. Sanarwar da bankin ya fitar yace kaso 46 na 'yan Najeriya watau mutane Miliyan 107 sun fada cikin talauci inda suke rayuwa a kasa da Dala $2.15 a kullun. Bankin yace ma'aikata basa samun rayuwa me kyau saboda Albashinsu baya kai musu yanda ya kamata. A baya dai bankin yace akwai Talauci sosai a tsakanin kauyawan Najeriya.