Monday, April 14
Shadow

Author: Auwal Abubakar

An min Wahayi, Allah ya gayamin kada in sake in aske gashin kaina>>Inji Fasto Jimmy Odukoya bayan da ake ta kiraye-kirayen ya aske kitson da yayi a kansa

An min Wahayi, Allah ya gayamin kada in sake in aske gashin kaina>>Inji Fasto Jimmy Odukoya bayan da ake ta kiraye-kirayen ya aske kitson da yayi a kansa

Duk Labarai
Fasto Jimmy Odukoya na cocin Fountain of Life church ya bayyana cewa, An masa wahayi inda Allah ya gaya masa kada ya sake ya aske gashin kansa. Faston ya bayyana wa mabiyansa hakane a gaban mabiyansa yayin da yake musu wa'azu. Yace kanwarsa ta bashi shawarar aske gashin kansa musamman saboda kada mutane su rika masa wani irin kallo. Saidai yace bai yanke shawara ba sai da ya nemi taimakon Allah kuma an masa wahayi inda aka ce kada ya aske gashin kan. Yace ya tura kanwar tasa ma yace ta je ta yi addu'a akai inda ta dawo tace itama an mata wahayi cewa kada ya aske gashin kan nasa. Inda ya bata amsar cewa shima dama an gaya masa.
Kalli Bidiyo: A karshe dai Shaikh Adam Muhammad Albany Gombe yawa Dan Bello Tonon sililin da yace zai masa

Kalli Bidiyo: A karshe dai Shaikh Adam Muhammad Albany Gombe yawa Dan Bello Tonon sililin da yace zai masa

Duk Labarai
{"remix_data":[],"remix_entry_point":"challenges","source_tags":[],"origin":"unknown","total_draw_time":0,"total_draw_actions":0,"layers_used":0,"brushes_used":0,"photos_added":0,"total_editor_actions":{},"tools_used":{},"is_sticker":false,"edited_since_last_sticker_save":false,"containsFTESticker":false} Sheikh Adam Muhammad Albany Gombe ya yiwa shahararren dan soshiyal Midiya, Dan Bello Tonon Sililin da ya yi Alkawarin yi masa. Hakan ya biyo bayan labarin da Dan Bello ya wallafa ne na zargin shugaban Izala, Sheikh Bala Lau da aikata ba daidai ba da dukiyar gina ajujuwan karatu. A martanin Sheikh Adam yace Dan Bello bashi da alaka da wani babban malami ko makaranta dan haka bai ga dalilin da zai sa wanda bashi da ilimin addini mutane su rika daukar labari daga wajansa ba. htt...
Bana Nuna Bangaranci a gwamnatina, Nafi baiwa ‘yan Arewa mukami fiye da ‘yan Kudu>>Shugaba Tinubu

Bana Nuna Bangaranci a gwamnatina, Nafi baiwa ‘yan Arewa mukami fiye da ‘yan Kudu>>Shugaba Tinubu

Duk Labarai
Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya bayyana cewa, baya nuna bangaranci a gwamnatinsa inda yace ya fi baiwa 'yan Arewa mukami fiye da 'yan kudu. Shugaban ya bayyana hakane ta bakin kakakinsa Sunday Dare. Yace Shugaba Tinubu ya baiwa 'yan Arewa 71 mukami a ma'aikatun gwamnatin tarayya daban-daban sannan ya baiwa 'yan kudu su 63 mukamai. Yace ko lokacin yana gwamnan Legas, Shugana Tinubu ya haiwa wanda ba 'yan legas ba mukami a gwamnatinsa. Sannan yace har yanzu gwamnati bata kare ba, za'a ci gaba da bayar da mukamai nan gaba.
Allah Sarki:Kalli Hotuna yanda tankin ajiyar ruwa ya fado mata tana bacci ta Mùtù

Allah Sarki:Kalli Hotuna yanda tankin ajiyar ruwa ya fado mata tana bacci ta Mùtù

Duk Labarai
Wannan wata matashiyace da Tankin Ajiyar ruwa da ake ajewa a sama ya fado mata ta mutu yayin da take bacci. Lamarin ya farune a Lekki, Lagos inda mutane da yawa ke ta nuna alhini kan lamarin. Matashiyar me suna Cynthia Oguzie ba ta dade da shiga gidan da kama haya ba. Tankin Ruwan dai ya ratsa rufin dakinta inda ya sauka akan gadonta. An bayyana wadda ta rasu din a matsayin 'yar shekaru 30.
A daina kokarin mayar mana da kasar mu kasar bakaken fata, mu ba bakar fata bane>>Inji Kasar Libya

A daina kokarin mayar mana da kasar mu kasar bakaken fata, mu ba bakar fata bane>>Inji Kasar Libya

Duk Labarai
'Yan kasar Libya sun fitar da sanarwa inda suka bayyana cewa, a daina kokarin mayar musu da kasarsu kasar Bakar Fata dan kuwa su ba bakar fata bane. Sun fitar da wannan sanarwa inda suke martani da kungiyoyin agaji na Duniya ciki hadda majalisar Dinkin Duniya kan sanarwar da suka fitar dake cewa, 'yan cirani su zauna a kasar ta Libya. Kungiyoyin Doctors Without Borders, the UN refugee agency, da Norwegian Refugee Council duk sun nemi bakaken fata 'yan Cirani dasu zauna a kasar ta Libya. Saidai kasar ta Libya tace hakan na barazanar mayar da kasar ta bakaken fata. 'Yan cirani da yawa ne dai ke bi ta cikin kasar ta libya dan ahiga kasashen Turai neman ayyukan yi. A baya dai kasar Tunisia ta taba yin irin wannan magana wadda tasa aka soketa a matsayin nuna kyamar bakake.
Mijinane baya kulani:Inji Wannan malamar da aka kama tana lalatawa dalibinta tarbiyya ta hanyar aika masa hotunan Batsà da yin lalata dashi

Mijinane baya kulani:Inji Wannan malamar da aka kama tana lalatawa dalibinta tarbiyya ta hanyar aika masa hotunan Batsà da yin lalata dashi

Duk Labarai
Wannan malamar makarantar me suna Emily Nutley an kamata tana lalatawa dalibinta tarbiyya ta hanyar tura masa hotunan batsa da yin lalata dashi. Malamar dai na aikin koyarwa ne a makarantar St. Xavier High School dake garin Cincinnati na jihar Ohio. An sakata ta rika kula da dalibai wanda basu da kokari sosai da makinsu bai da yawa. Inda a nan ne ta hadu da dalibin me shekaru 17. Ta fara aika masa sakonnin soyayya da hotunan batsa bayan an tashi daga karatu inda daga karshe dai har ta kai ga sun yi lalata. Dalibin dai a karshe ya nemi su daina abinda suke amma ta kiya. A karshe dai an kamata inda ta amsa laifinta. Rahotanni daga kafar Fox19 NOW sun ce zata iya fuskantar daurin shekaru 10 a gidan yari.
Attajirin Najeriya, Aliko Dangote ya cika shekaru 68 a yau

Attajirin Najeriya, Aliko Dangote ya cika shekaru 68 a yau

Duk Labarai
A yau ne attajirin dan kasuwa, Aliko Dangote ke cika shekaru 68 da Haihuwa. An haifi Dangote a ranar April 10, 1957 a garin Kano. Mahaifiyarsa Mariya Sanusi Dantata jikace a wajen Attajirin dan kasuwa, Alhassan Dantata. Mahaifinsa, Mohammed Dangote abokin kasuwancin Alhassan Dantata ne. Dangote yayi karatu a jami'ar Al-Azhar ta birnin Cairo na kasar Egypt. Bayan nan ne ya fara yiwa kawunsa Abdulkadir Sanusi Dantata aiki inda daga baya ya karbi bashin $3000 yana da shekaru 21 ya fara kasuwanci. Dangote yace tun yana makarantar Firamare ya fara kasuwanci.
Kalli Bidiyo, Saurayi ya dirkawa Budurwarsa ciki saidai ta gano cewa ashe ba ita kadai bace, yanzu haka wata budurwar ma na dauke da cikinsa

Kalli Bidiyo, Saurayi ya dirkawa Budurwarsa ciki saidai ta gano cewa ashe ba ita kadai bace, yanzu haka wata budurwar ma na dauke da cikinsa

Duk Labarai
Wata budurwa da saurayinta ya dieka mata ciki ta je asibi dan yin awo ta ga abin mamaki. Dan kuwa tana zaune sai ta ga saurayin nata da wata budurwa wadda itama ya dirka mata ciki ya rakata zuwa awo. Abinda ya baiwa budurwar ta farko mamaki shine shi da mahaifiyarsa a gidata suke zaune amma zai mata wannan cin amana. Kalli Bidiyon kasa: https://www.youtube.com/watch?v=wjDUf8fYnEM Me zaku ce akan wanan lamari?
Samun Soyayyar Rahama Sadau, Ya Fi Samun Naira Milyan Dari, Ra’ayin Hon Ibrahim Ajeebo

Samun Soyayyar Rahama Sadau, Ya Fi Samun Naira Milyan Dari, Ra’ayin Hon Ibrahim Ajeebo

Duk Labarai
{"remix_data":[],"remix_entry_point":"challenges","source_tags":[],"origin":"unknown","total_draw_time":0,"total_draw_actions":0,"layers_used":0,"brushes_used":0,"photos_added":0,"total_editor_actions":{},"tools_used":{},"is_sticker":false,"edited_since_last_sticker_save":false,"containsFTESticker":false} Samun Soyayyar Rahama Sadau, Ya Fi Samun Naira Milyan Dari, Ra'ayin Hon Ibrahim Ajeebo Me za ku ce?
Ji labarin yanda wata ta mutu ta dawo a jihar Kano

Ji labarin yanda wata ta mutu ta dawo a jihar Kano

Duk Labarai
BABBAR MAGANA: Tun Cikin Azumi Aka Yi Zaton Ța Mùtu Sai Gashi Ta Dawò Gida, Ashe Ba Ita Ta Mùťù Bà. Billahillazi yanzu a daren nan aka kawo min wani labari a cikin garin Kura dake Kano Wallahi Tallahi wai wata yarinya ce Allah Ya yi mata rasuwa tun a cikin azumi sai yau aka ganta kawai ta dawo gida luma Wallahi ita ce. Ni ma ina zaune ina cin abinci aka zo ana fada min ban yadda ban gama cin abincin ba na tashi na je domin na gani da idona. Wallahi ina zuwa har unguwar tasu kawai na ga kofar gidan su yarinyar cike da mutane na ta shiga ana ganinta. Ni ma na ganta Wallahi abun dai akwai mamaki sosai. Abu kamar a fim mutum ya mutu amma ya dawo. Adreshin unguwar da yarinyar take Alkalawa ne a cikin garin Kura dake Kano. Amma dai abun akwai mamaki sosai Wallahi. Ikon Allah. ...