Saturday, March 22
Shadow

Author: Auwal Abubakar

Addini Sauki Gareshi:Ko Tuntunbe ka yi zaka iya ajiye Azumi>>Inji Young Sheikh

Addini Sauki Gareshi:Ko Tuntunbe ka yi zaka iya ajiye Azumi>>Inji Young Sheikh

Duk Labarai
Young Sheikh dake Tafsirin Azumin watan Ramadan a birnin Zazzau na jihar Kaduna ya bada fatawar cewa ko tuntube mutum yayi zai iya ajiye Azumi. Yace ko ciwo mutum yaji ma zai iya ajiya Azumin dan an ce wanda bashi da lafiya ko matafiyi an sauwaka masa ya ajiye azumi idan Ramadan ya wuce ya rama. Yace wannan hukunci shima zai iya hawa kan wanda yayi Tuntube. Kalli Bidiyon anan
Ku gama hauragiyarku, Tabbas, Babu tantama Tinubu ne zai sake zama shugaban kasa a 2027>>Inji Shugaban APC, Ganduje

Ku gama hauragiyarku, Tabbas, Babu tantama Tinubu ne zai sake zama shugaban kasa a 2027>>Inji Shugaban APC, Ganduje

Duk Labarai
Shugaban jam'iyyar APC, Dr. Abdullahi Umar Ganduje ya bayyana cewa 'yan Adawa su gama duk wata hadaka da zasu yi, Tabbas Tinubu ne zai sake zama shugaban kasa a shekarar 2027. Ya bayyana hakane ta bakin me magana da yawu sa, Oliver Okpala. Ganduje yace hadakar SDP, Labour Party da PDP babu inda zata je dan kuwa kowane daga cikinsu yana da ra'ayi dabanne dan haka ba zasu samu matsaya ba. Ya bayyana 'yan Adawar a matsayin masu son kansu maimakon kishin al'umma.
Karyace:Fubara ya mayarwa da shugaba Tinubu martani bayan da yace bai tabuka komai ba yayin da aka kaiwa Bututun man fetur din Najeriya hari

Karyace:Fubara ya mayarwa da shugaba Tinubu martani bayan da yace bai tabuka komai ba yayin da aka kaiwa Bututun man fetur din Najeriya hari

Duk Labarai
Gwamnan jihar Rivers da shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya dakatar, Simi Fubara ya bayyana cewa ba gaskiya bane ikirarin da shugaban kasa yayi na cewa bai tabuka komai ba kan matsalar tsaron da ta kunno kai a jihar. Ya kuma karyata ikirarin shugaban kasar na cewa ya rushe majalisar jihar Rivers ba tare da gina wata ba. A martanin da ya mayar ta hannun me magana da yawunsa,Nelson Chukwudi Gwamna Fubara ya bayyana cewa, abin mamakine fadar shugaban kasar na magana akan abinda basu da masaniya akansa. Yace ko da yake ya dora Alhakin hakan akan masu baiwa shugaban kasar bayanai wanda sune suka kasa bashi bayana da ya kamata yayi amfani dasu wajan yin shawara. Fubara yace maganar da tsohon gwamnan jihar, kuma ministan Abuja a yanzu, Nyesome Wike yayine tasa aka kai harin. Yace ...
Nine kadai zan iya kawowa kasarnan ci gaba, Hadakar Atiku, El-Rufai, Rotimi Amaechi, da Peter Obi taron mutanene wanda ke son kansu kawai ba son Al’umma ba>>Inji Tinubu

Nine kadai zan iya kawowa kasarnan ci gaba, Hadakar Atiku, El-Rufai, Rotimi Amaechi, da Peter Obi taron mutanene wanda ke son kansu kawai ba son Al’umma ba>>Inji Tinubu

Duk Labarai
Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya bayyana hadakar da manyan 'yan Adawa suka yi da taron wanda damuwa tawa yawa. Ya bayyana hakane ta bakin kakakinsa, Bayo Onanuga. Hakan na zuwane bayan da Atiku Abubakar, Nasiru Ahmad El-Rufai, Rotimi Amaechi, Peter Obi, Kayode Fayemi da sauransu suka hada kai suka ce zasu kayar da Tinubun a zaben shekarar 2027. Sanarwar ta fadar shugaban kasa ta bayyana hadakar 'yan Adawar da cewa masu son kansu ne kawai ba masu kishin al'umma ba. Ya kuma bayyana cewa ci gaban kasa ne Bola Ahmad Tinubu ya saka a gaba, kuma shi kadai ne zai iya kawo ci gaban dan haka ba zai bari wasu taron sakarkaru su dauke masa hankali game da aikin da yake ba.
A karshe dai bayan da ya sha suka, Shima Kwankwaso ya fitar da Nasa Allah wadai din ga dakatarwar da Shugaba Tinubu yawa Gwamnan jihar Rivers

A karshe dai bayan da ya sha suka, Shima Kwankwaso ya fitar da Nasa Allah wadai din ga dakatarwar da Shugaba Tinubu yawa Gwamnan jihar Rivers

Duk Labarai
Tsohon gwamnan Kano, Dr. Rabiu Musa Kwankwaso ya bayyana rashin amincewarsa da dakatar da gwamnan jihar Rivers da shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya yi. Saidai bayyana ra'ayin nasa na zuwane bayan da ake ta tambayar ina ya shigene yayin da ake jin ta bakin manyan 'yan Adawa akan lamarin? Kwankwaso yace ya dakata ne ya ga wanda ke da ruwa da tsaki a cikin lamarin sun yi abinda ya dace shiyasa yayi shiru bai ce komi ba da farko. Saidai yace a yanzu yana Allah wadai da wannan mataki inda yace majalisar tarayya ta zama 'yan amshin shata da ba'a taba samun kamarsu ba a tarihin mulkin Najeriya. Yace sune ya kamata su rika dawo da shugaban kasa kan hanya idan ya aikata ba daidai ba amma gashi sun zama 'yan amshin shata. Kwankwaso yace shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya mayar da ...
Tonon silili: An gano cewa Dala Biliyan $3 aka rabawa Sanatoci suka amince da dakatar da gwamnan jihar Rivers, inda wasu sanatocin suka samu dala dubu 10 wasu suka samu dala dubu 5

Tonon silili: An gano cewa Dala Biliyan $3 aka rabawa Sanatoci suka amince da dakatar da gwamnan jihar Rivers, inda wasu sanatocin suka samu dala dubu 10 wasu suka samu dala dubu 5

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa, dala Miliyan $3 ce aka ware aka rabawa sanatocin Najeriya dan su amince da dakatarwar da shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu yawa gwamnan jihar Rivers, Simi Fubara. Rahoton yace a gidan Kakakin majalisar, Godswill Akpabio aka raba wadannan kudade a tsakannin ranekun Talata da Laraba. Rahoton yace wasu daga cikin sanatocin sun samu dala dubu $10 inda wasu suka samu dala Dubu $5 ya danganta da girman mukamin sanata. Rahoton ya kara da cewa Akpabio ya kira wasu sanatoci musulmai zuwa gidansa shan ruwa inda anan ne ya basu kasonsu, saidai wasu sanatoci ciki hadda tsohon gwamnan jihar Sokoto, Aminu Waziri Tambuwal basu amsa wannan gayyata ba. Rahoton yace Wike ne ya baiwa Kakakin majalisar Dattijai Godswill Akpabio kudaden da aka raba.
Shugaba Tinubu ya godewa Majalisar Tarayya saboda amincewa da dakatar da Gwamnan Rivers da suka yi

Shugaba Tinubu ya godewa Majalisar Tarayya saboda amincewa da dakatar da Gwamnan Rivers da suka yi

Duk Labarai
Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya godewa Majalisar tarayya bisa amincewa da dakatar da gwamnan jihar Rivers, Simi Fubara da yayi. Shugaban yace yana godiya musamman ga shuwagabannin majalisar, Kakakin majalisar Dattijai Godswill Akpabio dana majalisar Wakilai, Tajudeen Abbas. Sannan yace yana godiya ga sauran manyan 'yan majalisar dama duka 'yan majalisar. Shugaban ya kuma ce yana godiya ga 'yan Najeriya da suka bashi goyon baya bisa wannan lamari. Ya bayyana cewa yana fatan nan da wata 6 din da aka dakatar da gwamnan da majalisar a samu sulhu tsakanin wadanda basa jituwa. Shugaba Tinubu yace fadan jihar Rivers yana barazanane ga tattalin arzikin Najeriya shiyasa suka dauki matakin da suka dauka. Ya sha Alwashin ci gaba da hada kai da majalisar tarayya dan kawo ci gaba ...
A watan Maris matasa masu bautar kasa zasu fara karbar Alawus din Naira dubu 77>>Inji NYSC DG

A watan Maris matasa masu bautar kasa zasu fara karbar Alawus din Naira dubu 77>>Inji NYSC DG

Duk Labarai
Hukumar kula da masu bautar kasa a Najeriya, NYSC ta baiwa matasa masu bautar kasar tabbacin cewa, a watan Maris zasu fara ganin karin Alawus zuwa Naira 77,000. Shugaban hukumar, Brigadier General Olakunle Oluseye Nafiu ne ya bayyana hakan a yayin ganawa da matasan masu bautar kasa a ranar Alhamis. An yi taron ganawar ne a Wuse da Garki a Abuja. Brigadier General Nafiu ya bayar da tabbacin cewa Gwamnatin tarayya da Hukumar ta NYSC na kokarin ganin sun jiyawa matasan masu bautar kasa dadi.
Majalisar Dattawa ta amince da ayyana dokar ta-ɓaci a jihar Rivers

Majalisar Dattawa ta amince da ayyana dokar ta-ɓaci a jihar Rivers

Duk Labarai
Majalsiar Dattawa ta amince da dokar ta-ɓaci da shugaban Najeriya, Bola Tinubu ya ayyana a kan jihar Rivers a ranar Talata. Majalisar dai ta shiga tattaunawar sirri bayan da shugaban majalisar Godswill Akpabio ya karantar wasiƙar a zauren. Shugaban masu rinjaye na majalisar, Sanata Opeyemi Bamidele ne ya karanta buƙatar shiga tattaunawar ta sirri bisa dogaro da doka mai 135 ta kundin majalisar. Shugaban marasa rinjaye, Sanata Abba Moro ne ya amince da shiga ganawar sirrin. Da ma dai majalisar wakilai ta amince da wannan dokar ta ta-ɓaci a ranar Alhamis.
Hukumar Nimet ta gargaɗi kan ɓullar cutar sanƙarau a Najeriya

Hukumar Nimet ta gargaɗi kan ɓullar cutar sanƙarau a Najeriya

Duk Labarai
Hukumar kula da yanayi ta Najeriya Nimet ta yi gargaɗin cewa wasu jihohin arewacin ƙasar na ƙara fuskantar barazanar ɓarkewar cutar sanƙarau. Nimet a cikin sanarwar da ta wallafa a shafinta na X, ta ce jihohin Sokoto da Kebbi da Zamfara da Katsina da Kano da Jigawa da Bauchi da Yobe da Gombe da kuma Borno su ne suka fi fuskantar barazanar. Hukumar ta kuma ce alamomin cutar sanƙarau sun haɗa da zazzaɓi mai zafi da ciwon kai mai tsanani da riƙewar wuya da amai, sai rashin son kallon haske da ruɗewa da kuma ƙuraje. Nimet ta kuma ƙara da cewa ana iya kamuwa da cutar da hanyar mu'amula da masu ɗauke da cutar da kuma shiga cunkoso, inda ta buƙaci alumma su yi rigakafi su wanke hannu su kuma gujewa kusantar masu cutar su kuma rufe bakinsu da hanci. Hukumar ta kuma yi kira ga alumma da...