Wannan mahaifin ya sayawa 'ya'yansa Wardrobe ta saka kaya da suka dade suna tambayarsa ya siya musu.
Ya nuna yanda kayan yaran nasa ke zube a kasa inda yace sun dade suna rokonsa ya sai musu inda zasu rika saka kayansu.
Yace ya dade yana son ya sai musu sai aka yi sa'a wani abokinsa yana son sayarwa ya kirashi yace ya saya.
An ga yaran nata murna bayan da suka dawo daga makaranta suka tarar da mahaifinsu ya saya musu Wardrobe din.
https://twitter.com/i/status/2012415996615700912
Dan tsohon shugaban kasa, Ibrahim 'Yaradua ya auri mace ta 3.
Hakan na zuwane shekaru 2 bayan da ya auri diyar tsohon shugaban hukumar Immigration Muhammad Babandede, watau Amira
Lamarin ya dauki hankula a kafafen sada zumunta.
An ga 'yan wasan Senegal sun isa garin Rabat inda a canne zasu buga wasansu da kasar Morocco ranar Lahadi wanda shine na karshe na daukar kofin AFCON.
Saidai zuwansu garin ba tare da jami'an tsaro ba ya jawo cece-kuce.
An dai gansu suna Turmutsutsu a cikin jama'a.
https://twitter.com/i/status/2012317459643052271
Wannan Bidiyon 'yan Kwankwasiyya ne yayin da suka yi tattaki zuwa gidan Kwankwaso a Kano dan nuna soyayya a gareshi.
Hakan na zuwane yayin da Abba Kabir Yusuf ke shirin komawa jam'iyyar APC.
https://twitter.com/i/status/2012130665404452865
Wannan Bidiyon yanda sojoji suka chashe ne a wajan Bikin Tunawa da 'yan mazan jiya da aka yi.
An jisu suna chashewa da wakar Prince Sulaiman me Sukus.
https://twitter.com/i/status/2012251374654763377
Rafali Jalal Jayed dan kasar Morocco ne aka nada ya hura wasan Najeriya da Egypt.
Lamarin ya dagawa 'yan Najeriya da yawa hankali inda wasu kw ganin ba lallai awa Najeriya adalci a wasan ba.
A ranar 17 ga watan Janairu ne dai za'a buga wasan inda za'a samu wanda zai zo matsayi na uku a tsakanin kasashen biyu a gasar AFCON.
A ranar Tunawa da 'yan mazan jiya, Gwamnan jihar Kebbi, Nasiru Idris ya hadu da wani soja da ya rasa hannunsa a wajan aiki.
An gabatar da sojan a wajan gwamnan, inda gwamnan yace a yiwa sojan hannun Roba, inda yace a masa me kyau, har yana tambaya duka nawa yake?
https://twitter.com/i/status/2012100209048977895
Saidai wannan lamari ya jawo cece-kuce inda masu sharhi suka zargi gwamnan da rashin nuna tausai ga sojan musamman ganin cewa ya rasa hannun nasa ne wajan yiwa kasa Hidima.
Masu Sharhin na ganin cewa ba maganar kudi kawai bace, ya kamata gwamnan ya nuna alhini da halin da sojan ke ciki.
Dan gidan Ministan ayyuka, Osborn Umahi ya fito takarar neman kujerar shugaban karamar hukumar.
Ya fito ne neman takarar kujerar Karamar hukumar Ohaozara ta jihar Ebonyi.
Magoya bayansa ne suka rakashi Ofishin APC inda ya sayi fom din takarar akan Naira Miliyan 30.
Dama dai a baya yawa mahaifinsa shugaban yakin neman zabe sannan kuma gwamnan jihar Ebonyi na yanzu, Francis Nwifuru ya bayyana shi a matsayin dan takararsa
Wannan budurwar ta dauki hankula bayan da ta bayyana cewa, data auri Talaka, gara ta shekara 100 a gaban iyayenta.
Ta bayyana hakane a shafinta na Tiktok inda ta kara da cewa dan mahaifiyarta ta auri talaka ita ba zata auri talaka ba.
https://www.tiktok.com/@nanabilly_00/video/7595953476450946360?_t=ZS-9388RKvDR8z&_r=1