Tuesday, May 13
Shadow

Author: Auwal Abubakar

Ka Yi Gaggawar Janye Kalamanka Kan Dokar Haraji Domin Zai Tada Hankulan ‘Yan Kasa, Umarnin Fadar Shugaban Kasa Ga Gwamnan Bauchi

Ka Yi Gaggawar Janye Kalamanka Kan Dokar Haraji Domin Zai Tada Hankulan ‘Yan Kasa, Umarnin Fadar Shugaban Kasa Ga Gwamnan Bauchi

Duk Labarai
Ka Yi Gaggawar Janye Kalamanka Kan Dokar Haraji Domin Zai Tada Hankulan 'Yan Kasa, Umarnin Fadar Shugaban Kasa Ga Gwamnan Bauchi Gwamnatin tarayya ta ayyana kalaman Gwaman jihar Bauchi, Sanata Bala Muhammad, a matsayin kalaman tada hankulan 'yan kasa kan dokar fasalin haraji. Mai magana da yawun Shugaban kasa ne Sunday Dare, ne ya bayyana a shafin sa na twitter a safiyar yau Litinin. Daga Muhamma kwairi Waziri
YANZU YANZU: Hukumar DSS ta fara kama mutanen da suke ɗora Bidiyon Sojojin ƙasar Faransa da suke a Nigeria a kafafan Sada Zumunta, inda Yanzu haka Jami’an tsaron farin kaya (DSS) sun cafke ɗan gwagwarmaya Mahadi Shehu, bisa zargin yaɗa bidiyon Sojojin Faransa a shafinsa na X, da ke nuna cewa akwai masaukinsu a Nijeriya

YANZU YANZU: Hukumar DSS ta fara kama mutanen da suke ɗora Bidiyon Sojojin ƙasar Faransa da suke a Nigeria a kafafan Sada Zumunta, inda Yanzu haka Jami’an tsaron farin kaya (DSS) sun cafke ɗan gwagwarmaya Mahadi Shehu, bisa zargin yaɗa bidiyon Sojojin Faransa a shafinsa na X, da ke nuna cewa akwai masaukinsu a Nijeriya

Duk Labarai
DSS Ta Kama Mahdi Shehu Saboda yada Bidiyon sojojin Faransa. Hukumar tsaro ta farin kaya ta (DSS) ta kama Mahdi Shehu, mai fafutuka kuma mai sharhi kan al’amuran siyasa daga Kaduna. An Kama shi ne biyo bayan zargin da ake yi masa na yaɗa bidiyon sojojin Faransa a shafinsa na X. A cewar rahotanni, bidiyon ya nuna Shehu yana ikirarin cewa gwamnatin Najeriya tana shirin kafa sansanin sojojin Faransa a yankin Arewa maso Yamma, ikirarin da aka musanta. Mahdi yana hannun DSS a Kaduna, kuma akwai yiwuwar a gurfanar da shi a gaban kotu nan ba da jimawa ba. Hukumar DSS ta bayyana cewa sun tattauna da Mahdi kan rashin ingancin bayanan bidiyon kafin kama shi, amma tattaunawar ba ta kai ga nasara ba. Duk da haka, an umarci jami’an tsaro su mutunta haƙƙinsa yayin tsare shi.
Shugaba Buhari ya ce ba zai rubuta takarda ba kamar yadda sauran Shuwagabanni ke yi saboda gudun kada ya ɓatawa wasu mutane da iyalansu suna

Shugaba Buhari ya ce ba zai rubuta takarda ba kamar yadda sauran Shuwagabanni ke yi saboda gudun kada ya ɓatawa wasu mutane da iyalansu suna

Duk Labarai
Shugaba Buhari ya ce ba zai rubuta takarda ba kamar yadda sauran Shuwagabanni ke yi saboda gudun kada ya ɓatawa wasu mutane da iyalansu suna Mista Buhari ya ce ba zai yiwu ya rubuta takarda ba tare da ya ambaci sunayen wasu mutane ba wanda hakan ka iya jawo masu ɓacin rai ko bacin suna Me zaku ce?

Maganin yawan fushi

Magunguna
Yawan fushi matsala ce wadda idan mutum na da ita, zai yi fama da ma'amala da mutane. A wannan rubutu, zamu yi bayani dalla-dalla kan maganin yawan fushi dan kaucewa aikin dana sani. Idan kana da yawan Fushi, kada ka zama me yawan magana. Musamman a yayin da ranka ya baci, idan kace zaka yi magana, zaka yi dana sani akan abinda ka fada. Ka yi tunani, ko ka bari ka huce kamin kace wani abu, shima wanda ya maka ba daidai ba, ka barshi ya dawo hayyacinsa tukunna. Masana kiwon Lafiya sun bayyana cewa, idan ka yi fushi sosai, kuma ka kasa shawo kanka, to ka je ka motsa jiki, kamar tafiya da sauri ko yin gudu. Idan zai yiyu, ka samu guri kai kadai ka zauna ka nutsu na dan mintuna. Idan kai musulmi ne ka yawaita ziki, da karatun Qur'ani, zaka samu saukin lamarin. Hakanan idan a...
Tawagar Gwamna Ta yi hadari

Tawagar Gwamna Ta yi hadari

Duk Labarai
Tawagar Gwamnan Jihar Benue, Hyacinth Alia ta yi hadari a garin Ihugh dake karamar hukumar Vandeikya dake jihar Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa, Lamari ya farune ranar Lahadi inda shaidun gani da ido suka ce daya daga cikin motocin tawagar gwamnan ce ta buge wani mutum ya mutu. Lamarin ya farune yayin da gwamnan ya je gida yin hutun bikin kirsimeti. Lamarin ya faru sau biyu ne a yayin da gwamnan ke zuwa gida da lokacin da yake dawowa. Saidai me magana da yawun gwamnan, Solomon Iorpev ya musanta faruwar hadarin da tawagar gwaman, yace mota daya ce wadda aka bari a baya sauran motocin tawagar gwamnan sun wuce ta yi hadarin. An tuntubi kakakin 'yansandan jihar,  SP Catherine Anene, saidai bata ce komai akan lamarin ba.
Yanzu Adadin ‘Ya’yana Da Suka Sauke Kur’ani Sun Kai Biyar, Inji Jarumin Finfinan Hausa, Iliyasu Tantiri

Yanzu Adadin ‘Ya’yana Da Suka Sauke Kur’ani Sun Kai Biyar, Inji Jarumin Finfinan Hausa, Iliyasu Tantiri

Duk Labarai
Ga abinda Tantari ya bayyana bayan wasu yaransa biyu sun sauke Kur'ani "Alhamdulillah!!! Allah cikin Rahamarsa da amincewarsa, a yau Lahadi 29/12/2024 aka yi bikin saukar Karatun AL'QUR'ANI na ya'yana guda biyu, ABDULMUMIN ILYASU ABDULMUMIN DA RAHAMA ILYASU ABDULMUMIN. "Yanzu Yarana biyar kenan suka sauke QUR'ANI da Izinin Ubangiji cikin su takwas da Allah Ya ba ni, ina alfahari da murna da wadannan yara matuka. Ina godiya ga Allah S.W.T da ya ba ni ikon kulawa da su har suka kai wannan matsayi. Allah Ya sa su amfani musulunci da musulmai a duniya".
NNPCL ya ce matatar mai ta Warri ta koma aiki

NNPCL ya ce matatar mai ta Warri ta koma aiki

Duk Labarai
Kamfanin mai na gwamnatin Najeriya NNPCL ya ce matatar mai ta garin Warri na jihar Delta ta ci gaba da aiki. Shugaban NNPCL Mele Kyari ne ya bayyana hakan a yau Litinin yayin wani taron manema labarai da ya gudanar a matatar mai ƙarfin tace gangar mai 125,000 a kullum. "Duk da cewa ba 100 bisa 100 take aiki ba, muna kan aikin gyaran," in ji shi yayin da shugaban hukumar kula da harkokin mai na kamfanin Farouk Ahmed ke yi masa rakiya. "Mutane da yawa na tunanin yunƙurin namu ba gaskiya ba ne. Suna tunanin ba zai yiwu a aiwatar da abubuwa na ƙwarai a Najeriya ba, amma muna so ku gani da idonku." Matatar da ke yankin Ekpan na Warri, an ƙaddamar da ita a shekarar 1978 domin samar da mai ga jihohin kudancin Najeriya bisa kulawar kamfanin NNPCL . A cewar mai magana da yawun NNPCL,...
Gwamnatin Nijar ta kori kamfanonin sadarwa na Faransa

Gwamnatin Nijar ta kori kamfanonin sadarwa na Faransa

Duk Labarai
A Jamhuriyar Nijar, gwamnatin mulkin sojan kasar ta sanar da korar kamfanonin sadarwa na ƙasar Faransa na Camusat da Aktivko a duk faɗin ƙasar. Camusat na ɗaya daga cikin manyan kamfanonin sadarwa a Nijar, da kuma Aktivko wanda ya ƙware wajen samar da makamashi ga turakun sadarwa na wayoyin salula. Wannan na zuwa ne a loƙacin da hukumomin mulkin sojan Nijar ke ci gaba da korar kamfanonin Faransa daga Nijar a ƙoƙarin raba gari da ita baki daya. Wata sanarwa da Ministan Sadarwa Sidi Muhammad ya fitar ta ce an haramta wa dukkan 'yan ƙasa yin aiki tare da kamfanonin, amma babu wani cikakken bayanin dalilin da ya sa gwamnatin ta ɗauki matakin a yanzu. Sai dai masu lura da al'amuran yau da kullum a Nijar na cewa matakin ba zai rasa nasaba da tsaron ƙasa ba. A gefe guda kuma, masu ...
Babu yarjejeniyar yin karɓa-karɓa tsakanina da Atiku – Kwankwaso

Babu yarjejeniyar yin karɓa-karɓa tsakanina da Atiku – Kwankwaso

Duk Labarai
Tsohon gwamnan jihar Kano Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, ya musanta raɗe-raɗin da ke cewa an cimma yarjejeniya tsakaninsa da tsofaffin ƴan takarar shugaban ƙasa na jam'iyyun hamayyar ƙasar - Atiku Abubakar na PDP da Peter Obi na LP - kan cewa kowannensu zai yi mulki na wani wa'adi. A hirarsa da BBC, Kwankwaso ya ce bai san da maganar ba, amma ya samu labarin cewa ɓangaren Atikun na ta "yin taruka da shugabannin yankin ciki har da malamai, suna faɗa masu wannan magana".
Ni da ‘yan Najeriya muna cikin farin cikin gyara matatar mai ta Warri – Tinubu

Ni da ‘yan Najeriya muna cikin farin cikin gyara matatar mai ta Warri – Tinubu

Duk Labarai
Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya ce "shi da 'yan ƙasar suna cike da farin ciki" sakamakon gyara matatar mai ta garin Warri da kamfanin mai na NNPCL ya yi. Wani saƙo da shugaban ya wallafa a shafinsa na X ya ce "hakan zai ƙara wa 'yan Najeriya ƙwarin gwiwa kan fatan da suke da shi game da alƙawuran da muka yi". Ya ƙara da cewa labarin "hanya ce mai kyau ta kammala shekarar 2024 idan aka ƙara da nasarar da aka samu kan matatar mai ta Fatakwal". Yayin wani taron manema labarai a yau Litinin, shugaabn kamfanin NNPCL Mele Kyari ya bayar da sanarwar cewa sun gyara matatar kuma ta ci gaba da aiki a matakin kashi 60 cikin 100 na ƙarfinta. A cewar Tinubu: "Tun da yanzu matatar Warri na aiki bisa kashi 60 cikin 100, tsarin gwamnatina na samar da tabbataccen makamashi yana kan hanya. "...