Tuesday, December 16
Shadow

Author: Bashir Ahmed

Sanata Abubakar Sadiq Yar’adua ya fice daga jam’iyyar APC zuwa ADC

Sanata Abubakar Sadiq Yar’adua ya fice daga jam’iyyar APC zuwa ADC

Duk Labarai
Sanata Abubakar Sadiq Yar’adua wanda ya wakilci mazabar Katsina ta tsakiya a majalisar tarayya ya bayyana cewa, ya fice daga jam'iyyar APC zuwa jam'iyyar ADC. A takardar da ya aikewa da mazabarsa ranar 28 ga watan Yuli, Tsohon Dan majalisar ya bayyana cewa, tsare-tsaren jam'iyyar APC sun jefa al'umma cikin halin kaka nika yi. Yace da gaskene kalaman Malam Nasir El-Rufa’i da yace gwamnatin Tinubu ta koma 'yan Bindigar birni. Abubakar Sadiq 'Yar'Adua wanda yayi takarar gwamnan jihar Katsina a zaben 2023 yace Gwamnatin Tinubu na biyewa Turawa ne wanda burinsu tara Duniya yana jefa 'yan Najeriya a wahala. Yace yana fatan shi da mabiyansa zasu koma jam'iyyar ADC nan gaba kadan
Karya ake mana, Bamu ce Muna goyon bayan Tinubu a zaben shekarar 2027 ba>>Tsaffin ‘Yan Majalisar tarayya

Karya ake mana, Bamu ce Muna goyon bayan Tinubu a zaben shekarar 2027 ba>>Tsaffin ‘Yan Majalisar tarayya

Duk Labarai
Tsaffin 'yan majalisar tarayya sun bayyana cewa, ba gaskiya bane kudin goro da aka musu aka ce wai suna goyon bayan shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu a zaben shekarar 2027. Tsaffin 'yan majalisar sun yi taronsu a Abuja wanda shugaban ma'aikatan fadar shugaban kasa, Femi Gbajabiamila ya shirya inda ya roki takwarorinsa daga Arewa su marawa shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu baya a zaben shekarar 2027. Yace ko dan shugaban kasar ya kammala ayyukan ci gaba da ya faro a Arewa, ya kamata su mara masa baya. Bayan taron an fitar da sanarwa dake cewa, tsaffin 'yan majalisar sun amince su marawa shugaba Tinubu baya. Saidai wasu daga cikin tsaffin 'yan majalisar bisa jagorancin Rufa'i Chanchangi sun bayyana cewa ba gaskiya bane wannan ikirari. 'Yan majalisar da suka ce basu tare da Tinub...
Innalillahi wa’inna ilaihi raji’un: Saliha Idris Bintu ta fim din ‘Yan Zamani ta rigamu gidan gaskiya

Innalillahi wa’inna ilaihi raji’un: Saliha Idris Bintu ta fim din ‘Yan Zamani ta rigamu gidan gaskiya

Duk Labarai
Tauraruwar fina-finan Hausa, Saliha Idris Bintu wadda ta fito a fim din 'yan Zamani ta rasu. Rahotanni sunce ta rasu ne a Ranar Lahadi kuma tuni aka yi jana'izar ta kamar yanda addinin musulunci ya tanada. Rahotanni sun yi yawa a kafafen sada zumunta cewa, ta rasu inda akaita wallafa hotunan ta da sakonnin ta'aziyya. https://www.tiktok.com/@maayyadee/photo/7534267082750414085?_d=secCgYIASAHKAESPgo8%2Bi7rhzJ2rvPFN0skFeRrj0s1yh5gnmI%2BVBkJXpi8KFEXvh9XXwEzuMrvAovzVp4OBqg85Y8gmnK2AQ98GgA%3D&_r=1&_svg=1&aweme_type=150&checksum=ad27d0ba2b0bf0a15518815f6f4927269dff1e0a2fd089bcde06bd86b4978cca&link_reflow_popup_iteration_sharer=%7B%22click_empty_to_play%22%3A1%2C%22dynamic_cover%22%3A1%2C%22follow_to_play_duration%22%3A-1.0%2C%22profile_clickable%22%3A1%7D&pic_cnt...
Da Duminsa:Mummunan Hadarin Mota ya rutsa da Tauraruwar Kannywood, Samha M. Inuwa, Kalli Bidiyon

Da Duminsa:Mummunan Hadarin Mota ya rutsa da Tauraruwar Kannywood, Samha M. Inuwa, Kalli Bidiyon

Duk Labarai
Rahotanni na cewa, Mummunan Hadarin mota ya rutsa da Tauraruwar Kannywood, Samha M. Inuwa. Hakan ya farune yayin da take kan hanyarta ta komawa Kano daga wajan bikin data halarta a Kaduna. Motar su Samha ta daki Trela ne ta baya wanda yasa ta lalace. Gfresh Al-amin ya bayyana cewa sun yi waya kuma ta sanar dashi tana bukatar addu'a. https://www.tiktok.com/@gfreshfanpage/video/7534450951780945158?_t=ZS-8ya5jYjHVa5&_r=1 Shima Hassan Make-Up ya wallafa hotunan Samha yana kuka da kiran a sakata a addu'a. https://www.tiktok.com/@officielhassanmakeup227/video/7534477043191319813?_t=ZS-8ya5pDXXDXs&_r=1
Idan Tinubu ya sake cin zabe, Najeriya ba zata kai Labari ba, Inji Malam Nasiru Ahmad El-Rufai

Idan Tinubu ya sake cin zabe, Najeriya ba zata kai Labari ba, Inji Malam Nasiru Ahmad El-Rufai

Duk Labarai
TIRƘASHI: Zai yi Wuya Nijeriya ta Ci Gaba da Rayuwa Idan Tinubu ya Zarce a 2027 - El-Eufai Tsohon Gwamnan Jihar Kaduna, kuma Korarren Ministan da majalisa ta ƙi tantance wa, Malam Nasir El-Rufai , ya bayyana cewa makomar Najeriya na cikin hadari idan jam’iyyar APC ta ci gaba da mulki bayan 2027. Jaridar Sahara Reporters ta rawaito cewa El-Rufai ya bayyana hakan ne a Sakkwato yayin wani gangamin wayar da kan jama'a na jam’iyyar hamayya ta hadaka, African Democratic Congress (ADC), inda ya ce yana cikin siyasa ne don ceto kasa, ba don wata riba ba. Ya ce ya fice daga APC ne saboda gazawarta wajen tafiyar da mulki, yana mai gargadin cewa ci gaban mulkin APC zai iya rusa tubalin zamantakewa na kasar. El-Rufai, wanda yanzu ke daya daga cikin jiga-jigan ADC, ya sha alwashin hada ...
Kalli Bidiyo: Lokacin ina da kudi, matana 4 amma dana Talauce duk sun barni>>Inji Mai Dawayya

Kalli Bidiyo: Lokacin ina da kudi, matana 4 amma dana Talauce duk sun barni>>Inji Mai Dawayya

Duk Labarai
Tauraron mawakin Hausa, Aminu Mai Dawayya ya bayyana cewa a lokacin yana da budi, matansa 4. Ya bayyana hakane a wata hira da RFIHausa suka yi dashi. Ya bayyana cewa, Amma da kudinsa suka kare, duk sai kowa ya tafi ya barshi Yace Asalin dalilin da yasa ake ce masa Mai Dawayya shine shi masoyin Rukayya Dawayya ne da Ali Nuhu kuma asalin sanarsa Achaba ne. https://www.tiktok.com/@rfi_ha/video/7534272889013554488?_t=ZS-8ya2tLAjmzo&_r=1
Serap ta ba wa gwamnan Neja wa’adin janye umarnin rufe rediyon Badeggi FM

Serap ta ba wa gwamnan Neja wa’adin janye umarnin rufe rediyon Badeggi FM

Duk Labarai
Ƙungiyar neman shugabanci na gari ta Serap ta bai wa gwamnan jihar Neja da ke arewacin Najeriya wa'adin awa 48 domin ya janye umarnin rufe gidan rediyon Badeggi FM ko kuma ya fuskanci matakin shari'a. Cikin wata wasiƙa da ƙungiyar ta aika wa Gwamna Umaru Bago, shugaban Serap Kolawole Oluwadare ya ce rufe gidan rediyon da ke birnin Minna "saɓa wa doka" ne, kuma ya nemi gwamnan ya mayar musu da lasisinsu. "Toshe bakin masu suka da sunan tsaron ƙasa keta rantsuwar kama aiki da ka yi ne da kuma ɓata sunan Najeriya a idon duniya game da haƙƙin ɗan'adam," a cewar wasiƙar. A ranar Juma'a ne Gwamna Bago ya bayar da umarnin rufe gidan rediyon na Badeggi FM nan take tare da ƙwace lasisinsa saboda zargin "tayar da fitina".
Kalli Bidiyo: Abin takaici ne yanda aka baiwa ‘yan mata ‘yan kwallon Najeriya kyautar Naira Miliyan 160, kudin da har soja ya gama aikinsa in za’a hada duka abinda zai samu ba zai kai hakan ba>>Soja ya koka

Kalli Bidiyo: Abin takaici ne yanda aka baiwa ‘yan mata ‘yan kwallon Najeriya kyautar Naira Miliyan 160, kudin da har soja ya gama aikinsa in za’a hada duka abinda zai samu ba zai kai hakan ba>>Soja ya koka

Duk Labarai
Sojan Najeriya ya koka bisa yanda aka baiwa 'yan mata 'yan kwallon Najeriya kyautar Miliyoyin kudade da gidaje bayan sun lashe kofij gasar kwallon mata ta Afrika. Sojan yace duka aikin da suka yi bai wuce na watanni 3 ba. Yace amma abin takaici shine kudaden da aka basu tun daga randa aka dauki soja aiki har ya gama aikinsa ba zai samu irin wadannan kudaden ba. https://twitter.com/ChuksEricE/status/1951970780218060823?t=T8tOwYdS5fcx3MI5pgmKZQ&s=19