Saturday, April 25
Shadow

Author: Bashir Ahmed

Kalli Bidiyon: Shugaba Tinubu ya je gaishe da matar tsohon shugaban kasa, Muhammadu Buhari, watau A’isha a Kaduna

Kalli Bidiyon: Shugaba Tinubu ya je gaishe da matar tsohon shugaban kasa, Muhammadu Buhari, watau A’isha a Kaduna

Duk Labarai
Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya je gidan tsohon shugaban kasa, Muhammadu Buhari inda ya gaishe da matarsa, A'isha. Shugaban ya gaishe da A'isha ne inda yace mata zai ci gaba da tabbatar da irin tsare-tsaren shugaban kasa, Muhammadu Buhari. https://twitter.com/Abdool85/status/1969016925066858995?t=6E_jyQ2Plu96hHwEVx-jLA&s=19
Bayan na Farko, Matatar Man fetur din Dangote ta sake aika Jiragen Ruwa uku dauke da Gas zuwa kasar Amurka

Bayan na Farko, Matatar Man fetur din Dangote ta sake aika Jiragen Ruwa uku dauke da Gas zuwa kasar Amurka

Duk Labarai
Rahotanni sun ce matatar man fetur din Dangote ta sake aikewa da Manyan Jiragen ruwa dauke da Gas zuwa kasar Amurka. Hakan na zuwane bayan na farko da matatar ta kai kasar. Rahotannin sun ce kasar Amurka ta bayyana cewa, Gas din da matatar man fetur din Dangote ke fitarwa na da ingancin da kasar ke bukata. A baya dai mutane da yawa sun yi mamakin jin yanda matatar man fetur din Dangoten ta yi nasarar fara fitar da man fetur zuwa kasar Amurka.
Daga Shekarar 2026, Duk Naira dubu dari da Dan Najeriya ya samu, Gwamnatin Tarayya zata dauki Naira dubu goma sha biyar daga ciki a matsayin kudin haraji

Daga Shekarar 2026, Duk Naira dubu dari da Dan Najeriya ya samu, Gwamnatin Tarayya zata dauki Naira dubu goma sha biyar daga ciki a matsayin kudin haraji

Duk Labarai
Ko kun san cewa sabuwar dokar Haraji ta tanadi cewa daga shekarar 2026, Duk wanda ya samu 100 a matsayin kudin shiga, Gwamnati zata dauki Naira 15,000 a matsayin kudin Haraji? Dokar dai ta bayyana yawan kudin da za'a rika cirewa daga yawan kudin da mutum ya samu: First ₦800k: 0% Next ₦2.2M: 15% Next ₦9M: 18% Next ₦13M: 21% Next ₦25M: 23% Above ₦50M: 25%
Kalli Bidiyo: Cikin sahabban Annabi(Sallallahu Alaihi Wasallam) babu wanda ya rika cewa shi Ahalussunnah ne ya rika kafirta sauran sahabbai>>Inji Digital Imam

Kalli Bidiyo: Cikin sahabban Annabi(Sallallahu Alaihi Wasallam) babu wanda ya rika cewa shi Ahalussunnah ne ya rika kafirta sauran sahabbai>>Inji Digital Imam

Duk Labarai
Malamin addinin Islama, Digital Imam ya bayyana cewa, a cikin Sahabban Annabi(Sallallahu Alaihi Wasallam babu wadanda suka rika ikirarin Ahlussunah suka rika kafurta sauran Sahabbai. Malam yace ikirarin Ahlussunah daga baya ya fito. https://www.tiktok.com/@digital_imaam/video/7551058248858619143?_t=ZS-8zqp1hX5n05&_r=1
Kalli Bidiyo: Ta aikawa Malam ya baiwa Mijinta Hakuri bayan da ya hanata kudin anko da kudin gudummawar zuwa bikin kawarta amma ta sayar da buhun shinkafa ta tafi

Kalli Bidiyo: Ta aikawa Malam ya baiwa Mijinta Hakuri bayan da ya hanata kudin anko da kudin gudummawar zuwa bikin kawarta amma ta sayar da buhun shinkafa ta tafi

Duk Labarai
Wata mata da mijinta ya ki bata kudin gudummawa dana Anko zuwa wajan bikin kawarta ta sayar da buhun shinkafa ta yi hidimar bikin. Saidak bayan data dawo daga wajan bikin, ya dauke mata duka kayanta inda yace sai ta shekara 2 tana saka wadannan kayan kamin ya fito mata da kayanta. Tace ta gayawa mahaifinta kuma yace mijin yayi daidai. Shine ta aikawa malam ya baiwa mijin hakuri. https://www.tiktok.com/@mariamelhadjigomb/video/7550917552537423126?_t=ZS-8zqnVya4ktN&_r=1
Kalli Bidiyon yanda rikici ya barke tsakanin mawaki 442 da wata data zargi cewa watakila Baturiyar da yace ya musuluntar ba da gaske bane, Neman Trending ne

Kalli Bidiyon yanda rikici ya barke tsakanin mawaki 442 da wata data zargi cewa watakila Baturiyar da yace ya musuluntar ba da gaske bane, Neman Trending ne

Duk Labarai
Tauraron mawaki, 442 ya nuna bacin randa bayan da wata ta zargi cewa baturiya da yace yana son musuluntar da ita ba gaskiya bane. 442 dai yace wata baturiya da aka gansu tare tace tana son musulunta. Wata me suna Jaruma ta fito tace watakila neman trending ne 442 yake amma ta bashi shawarar ya kai baturiyar Masallaci a musuluntar da ita https://www.tiktok.com/@hassana.jaruma/video/7550586198067072278?_t=ZS-8zqFeG3rKFM&_r=1 Wannan magana ta batawa 442 rai inda yace da gaske ne maganar musuluntar Baturiyar. https://www.tiktok.com/@mr442_/video/7551398969784503570?_t=ZS-8zqFjb9psXJ&_r=1
Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu zai kai ziyara jihar Kaduna, Gobe Juma’a

Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu zai kai ziyara jihar Kaduna, Gobe Juma’a

Duk Labarai
Shugaban Kasa, Bola Ahmad Tinubu zai kai ziyara jihar Kaduna a gobe, Juma'a idan Allah ya kaimu. Shugaban zai halarci daurin auren dan Sanata Abdulaziz Yari me suna Nasirudeen Yari da amaryarsa, Safiyya Shehu Idris. Hakan na kunshene a cikin wata sanarwa da me magana da yawun shugaban kasar, Bayo Onanuga ya fitar a ranar 18 ga watan Satumba. Hakanan sanarwar tace shugaban kasar zai kuma kaiwa matar tsohon shugaban kasa, Marigayi Muhammadu Buhari ziyara. Sannan a Ranar Juma'ar dai ne shugaban zai koma Abuja.