Monday, April 20
Shadow

Author: Bashir Ahmed

Kalli Bidiyo: Inda Gwamna Abba Kabir Yusuf yace yana bayar da Naira Dubu 50 a rika baiwa matasa duk wata a wajan wani taro da ya halarta, saidai matasan sun ce ba’a basu ko sisi

Kalli Bidiyo: Inda Gwamna Abba Kabir Yusuf yace yana bayar da Naira Dubu 50 a rika baiwa matasa duk wata a wajan wani taro da ya halarta, saidai matasan sun ce ba’a basu ko sisi

Duk Labarai
Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf ya bayyana cewa daya daga cikin ayyukan da yakewa jihar Kano Shine baiwa matasa tallafin Naira dubu 50 a wata. Ya bayyana hakane a wajan wani taron siyasa. Saidai matasan sun musanta wannan ikirari na gwamnan inda suka ce ba'a basu ko sisi. Gwamnan dai yace zai yi bincike kan lamarin.
Matsalar tsaro ta janyowa Najeriya asarar Naira Tiriliyan 7.17 sannan kaso 40 na dabbobin da ake dasu sun salwanta saboda matsalar

Matsalar tsaro ta janyowa Najeriya asarar Naira Tiriliyan 7.17 sannan kaso 40 na dabbobin da ake dasu sun salwanta saboda matsalar

Duk Labarai
Wata Kungiya me sun, Agramondis Research and Consulting ta bayyana cewa matsalar Tsaro ta jawowa Najeriya asarar Naira Tiriliyan 7.17 sannan kaso 40 cikin 100 na dabbobin da ake dasu sun salwanta. Rahoton yace bangaren dabbobi na taimakawa da kaso 10 cikin 100 na ci gaban Najeriya sannan ya samarwa mutane Miliyan 4.5 aikin yi amma gwamnati bata zuba jari sosai a bangaren. Kungiyar tace fari, Canjin Yanayi da matsalar tsaro, da karancin ruwan sama da rikicin manoma da makiyaya na kawowa bangaren tsaikon ci gaba. Dan hakane ta yi kira ga gwamnatin tarayya ta kawo dauki a hangaren ta hanyar ilimantar da manoma da makiyaya da basu tallafi da kayan aiki na zamani
Gwamna Abba Kabir Ya Baiwa Matashin Yaro Mai Harkar Kere-Kere A Kano Jari Na Makuden Kudade Tare Da Daukar Nauyin Karatunsa

Gwamna Abba Kabir Ya Baiwa Matashin Yaro Mai Harkar Kere-Kere A Kano Jari Na Makuden Kudade Tare Da Daukar Nauyin Karatunsa

Duk Labarai
Gwamna Abba Kabir Ya Baiwa Matashin Yaro Mai Harkar Kere-Kere A Kano Jari Na Makuden Kudade Tare Da Daukar Nauyin Karatunsa. {"remix_data":[],"remix_entry_point":"challenges","source_tags":[],"origin":"unknown","total_draw_time":0,"total_draw_actions":0,"layers_used":0,"brushes_used":0,"photos_added":0,"total_editor_actions":{},"tools_used":{},"is_sticker":false,"edited_since_last_sticker_save":false,"containsFTESticker":false} Hazikin matashin nan mai harkar kere-kere, Injiniya Khalifa, ya samu tallafin makuden kudade daga wurin Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf domin ci gaba da harkar kere-kerensa kamar yadda ya jima yana ta neman jari. Haka kuma Gwamna zai dauki nauyin ci gaba da karatunsa. Daga Fauziyya D. Sulaiman
Kalli Hotuna: Yanda Sakkwatawa suka fito da yawa suka tarbi Tsohon Gwamnan jihar, Aminu Waziri Tambuwal bayan sakoshi daga hannun EFCC

Kalli Hotuna: Yanda Sakkwatawa suka fito da yawa suka tarbi Tsohon Gwamnan jihar, Aminu Waziri Tambuwal bayan sakoshi daga hannun EFCC

Duk Labarai
Sakkwatawa da yawa ne suka fito kwansu da kwarkwatarsu suka nunawa tsohon Gwamnan jihar, Aminu Waziri Tambuwal soyayya bayan da ya koma jihar bayan sakoshi daga hannin EFCC. Sanata Aminu Waziri Tambuwal ya shafe kwana daya a hannun EFCC inda suke zarginsa da cire Naira Biliyan 189 daga asusun bankin jihar ba bisa ka'ida ba. ADC ta yi zargin cewa, Bita da kullin siyasane yasa EFCC kama tsohon Gwamnan.
Kalli Bidiyon wani dan Izala da yaje Maulidi a kasar China, sabosa irin kayan abincin da aka shirya a wajan

Kalli Bidiyon wani dan Izala da yaje Maulidi a kasar China, sabosa irin kayan abincin da aka shirya a wajan

Duk Labarai
{"remix_data":[],"remix_entry_point":"challenges","source_tags":[],"origin":"unknown","total_draw_time":0,"total_draw_actions":0,"layers_used":0,"brushes_used":0,"photos_added":0,"total_editor_actions":{},"tools_used":{},"is_sticker":false,"edited_since_last_sticker_save":false,"containsFTESticker":false} Wani dan Najeriya da yace ba ruwansa da Maulidi a Najeriya, da ya je kasar China ya halarci Maulidi saboda irin yanda aka shiryashi. An ganshi a wajan Maulidin yana cin kayan abinci kala-kala. Da yawa dai sun ce da haka ake Maulidi a Najeriya da yawa sun rika halarta. https://www.tiktok.com/@elbildad/video/7538087905353305350?_t=ZS-8ytN08Tjp1U&_r=1
Kalli Bidiyo: Da APC da Gwamnatin jihar Kaduna na Tsyne musu Albarka, na barsu da Duniya>>Inji tsohon  Gwamnan Kaduna, El-Rufai

Kalli Bidiyo: Da APC da Gwamnatin jihar Kaduna na Tsyne musu Albarka, na barsu da Duniya>>Inji tsohon Gwamnan Kaduna, El-Rufai

Duk Labarai
Tsohon Gwamnan jihar Kaduna, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai ya bayyana cewa, Da Gwamnatin jihar Kaduna da Jam'iyyar APC ya tsine musu Albarka ya barsu da Duniya. Gwamnan ya bayyana hakane a wata hira da gidan rediyon Alheri yayi dashi inda yake cewa ko danka ne idan ka yi iya kokarinka sai ka tsine mishi Albarka ka barshi da Duniya. https://www.tiktok.com/@kusfa80usman/video/7538557884624342290?_t=ZS-8ytI09dnN7h&_r=1
Kalli Bidiyo: Shugaban kasa, Gwamnoni da ‘yan Majalisa duk mahaukata ne>>Inji Malam saboda ciwo bashi

Kalli Bidiyo: Shugaban kasa, Gwamnoni da ‘yan Majalisa duk mahaukata ne>>Inji Malam saboda ciwo bashi

Duk Labarai
Malam ya bayyana damuwarsa kan ciwo bashin da Gwamnati take inda yace Wadanda suka amince a ciwo bashin tun daga ka shugaban kasa, Gwamnonin da 'yan majalisa duk mahaukatane. Malam yace yawan bashin da ake bin Najeriya zai sakamu da 'ya'yan mu cikin matsala. https://www.tiktok.com/@zaidou1taza/video/7537794662770216248?_t=ZS-8ytElK9cITY&_r=1
Zuwa yanzu, Shugaba Tinubu ya shafe kwanaki 181 a kasashen waje tun bayan hawansa mulki

Zuwa yanzu, Shugaba Tinubu ya shafe kwanaki 181 a kasashen waje tun bayan hawansa mulki

Duk Labarai
Jam'iyyar ADC ta caccaki shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu saboda yawan tafiye-tafiyen da yake yi zuwa kasashen waje. Jam'iyyar ta bayyana hakane ta bakin kakakinta, Bola Abdullahi inda yace ana kashe kudaden Talakawa wajan tafiye-tafiyen shugaban kasar. Ya bayyana cewa, wannan shine karo 40 da shugaba Tinubu zai bar Najeriya tun bayan hawansa mulki kuma ya kwashe kwanaki 181 a kasashen waje. Sanarwar tace wannan kusan watanni 6 kenan da shugaba Tinubu ya kwashe a kasashen wajan. ADC tace tana Allah wadai da irin wadannan tafiye-tafiyen na shugaban kasa musamman ganin cewa babu wani abin ci gaba da hakan ya kawowa kasarnan.