Gwamnatin Nijeriya Ta Yi Maraba Da Naɗin Maryam Bukar Hassan A Matsayin Jakadiyar Zaman Lafiya Ta Duniya
Gwamnatin Nijeriya Ta Yi Maraba Da Naɗin Maryam Bukar Hassan A Matsayin Jakadiyar Zaman Lafiya Ta Duniya.
A yau Litinin ne gwamnatin shugaba Tinubu ta karɓi baƙuncin fitacciyar mai waƙar baka Maryam Hasan wadda ta yi nasarar zama jakadiyar zaman lafiya ta majalisar dinkin duniya. Mataimakin shugaban Najeriya Kashim Shettima ne ya karbi bakuncin jakadiyar da tawagarta a fadar shugaban ƙasa inda ya bayyana farincikin gwamnati da shirinta na yin aiki da jakadiyar yar asalin Najeriya don ƙarfafa zaman lafiya a Najeriya da ma duniya baki ɗaya.
Da yake jawabi ga tawagar ta Global Advocate for Peace ta Majalisar Dinkin Duniya, Shettima ya bayyana Maryam a matsayin mace mai tsayuwar daka wajen sadaukar da basirarta ga wanzar da zaman lafiya musamman a wata ƙasidarta mai taken 'Rikici bai...








