Saturday, December 13
Shadow

Author: Bashir Ahmed

Dattawan APC sun ce basu son Kwankwaso ya koma jam’iyyar

Dattawan APC sun ce basu son Kwankwaso ya koma jam’iyyar

Duk Labarai
Raɗe-raɗin dawowar Kwankwaso jam'iyyar APC mai mulki, na cigaba da fitowa fili. An samu rudani a sakateriyar jam’iyyar APC, a ranar Talata, bayan da Shugaban jam’iyyar na kasa, Dr. Abdullahi Umar Ganduje, da Ministan Jiha na Harkokin Gidaje da Ci gaban Birane, Yusuf Ata, suka yi sabani kan daowawar Kwankwaso jam'iyyar APC. Yayin da Minista Ata ke cewa Kwankwaso – wanda kuma tsohon Ministan Tsaro ne – ya rasa karbuwa a Kano kuma siyasar sa na dab da mutuwa, Ganduje ya ce APC ba lallai ta ki karbansa ba, yana mai cewa “aboki a lokacin bukata, aboki ne na gaskiya.” Ata, yayin da yake zantawa da manema labarai bayan ganawa da Ganduje a sakateriyar jam’iyyar da ke Abuja, ya bayyana cewa matsin lambar siyasar da Kwankwaso ke ciki ne ke sa shi kokarin dawowa APC, yana mai cewa har Kw...
Mutane sama da dari biyu sun karbi Musulunci

Mutane sama da dari biyu sun karbi Musulunci

Duk Labarai
Mutane Sama da 210 tare da ya'yansu Sun karbi Addinin Muslunci. Fiye da mutum 210 tareda ‘ya’yansu ne suka Karbi Addinin musulinci a kauyen (Jadebri) da ke karamar hukumar (Bandai) a Arewacin Ghana. Allah ya ɗaukaka Addinin Muslunci da Musulmai Sannan Ana Bukatar Kayi Sharing Zuwa group group domin Samun Addu'o'in Al'ummar Musulmai Allah ya Dawwamar dasu a Cikin Addinin Muslunci
Gwamnan Jihar Kano ya bayar da Naira Miliyan 15 dan a ci gaba da kulawa da me cutar daji, Halisa Muhd

Gwamnan Jihar Kano ya bayar da Naira Miliyan 15 dan a ci gaba da kulawa da me cutar daji, Halisa Muhd

Duk Labarai
Gwamna Abba Kabir Yusuf Ya Biyawa Halisa Muhd Naira Miliyan 15 Don Ci Gaba da Maganin Cututtukan da ke Damunta Mai girma Gwamnan Jihar Kano, Injiniya Abba Kabir Yusuf, ya sake nuna jajircewarsa wajen tallafawa marasa lafiya masu bukata ta musamman, inda ya biya Naira miliyan 15 domin ci gaba da maganin Halisa Muhd, wadda ke fama da cutar daji (cancer). Wannan kudin na daga cikin tallafin da Gwamnan ya bayar domin taimakawa Halisa Muhd wajen samun magani mai tsada, bayan da ya riga ya biya kudin aikin farko da aka yi mata. Fauziyya D. Sulaiman, Babbar Mai Ba Gwamna Shawara kan Harkokin Mabukata da Gajiyayyu, ta bayyana godiyarta ga Gwamnan bisa wannan taimako, tare da jaddada cewa gwamnatin Kano za ta ci gaba da tallafawa marasa lafiya da masu bukata ta musamman a jihar. Wannan ...
Atiku Abubakar ya bayyana cewa ba zai bar jam’iyyar PDP ba amma ya fadi dabarar da zasu yi amfani da ita dan kawar da Gwamnatin Tinubu

Atiku Abubakar ya bayyana cewa ba zai bar jam’iyyar PDP ba amma ya fadi dabarar da zasu yi amfani da ita dan kawar da Gwamnatin Tinubu

Duk Labarai
Madugun Adawar Siyasa A Najeriya kuma dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP a zaben 2023, Alhaji Atiku Abubakar, ya bayyana cewa yana nan daram a cikin jam’iyyar PDP, kuma ba shi da niyyar ficewa daga cikinta. Ya bayyana hakan ne a wata ganawa da mata mambobin Kwamitin Amintattu na jam’iyyar (BoT) da suka kai masa ziyara domin neman hanyoyin ceto jam’iyyar daga rushewa gaba daya. A cewar Atiku, rahotannin da ke cewa yana shirin barin PDP zuwa wata jam’iyya kamar SDP ba su da tushe balle makama, kuma an kirkire su ne domin rikita shirin kafa kawancen jam’iyyun adawa da ake yi. Ya jaddada cewa yana nan a matsayin cikakken memba na PDP, kuma yana jagorantar yunkurin kafa kawancen jam’iyyun adawa domin kalubalantar jam’iyyar APC a zaben 2027. A wata ganawa da aka yi a Abuja, Atiku y...
‘Yan Bìndìgà sun fi Sojojin Najeriya kayan aiki masu kyau>>Inji Majalisar tarayya

‘Yan Bìndìgà sun fi Sojojin Najeriya kayan aiki masu kyau>>Inji Majalisar tarayya

Duk Labarai
Majalisar wakilai ta bayyana cewa alamu na kara fitowa fili dake nuna mayakan Kungiyar Bòkò Hàràm sun fi sojojin Najeriya makamai masu kyau. Majalisar ta bayyana hakane a zamanta na ranar Talata inda ta bayyana damuwa matuka kan harin da ake zargin kungiyar ta Boko Hàràm da kaiwa a barikin sojoji ta Giwa dake jihar Borno. Majalisar tace wannan alamace karara dake nuna cewa mayakan kungiyar ta Bòkò Hàràm sun fi sojojin Najeriya makamai masu kyau. 'yan majalisar sun kuma bayyana damuwa kan yanda kungiyar ke dawowa a hankali da kuma asarar rayukan da ake samu a hare-haren da take kaiwa a jihohin Borno da Yobe. Duk da yawan kudin da gwamnati ke warewa bangaren tsaro na karuwa duk shekara, amma korafi na yawa a kan yawa ko ingancin makaman da ake siyowa sojojin. Misali a shekarar...

Bidiyo Da Duminsa: Kasar India ta Jefawa kasar Pakistan makami inda ya kàshè karamin yaro da jikkata mutane 2

Duk Labarai
Rahotanni daga Fakistan na cewa, Kasar India ta jefa mata makami inda ya kashe yaro ya jikkata mutane 2. Lamarin na zuwane yayin da ake tsaka da yakin cacar baki tsakanin kasashen biyu. Saidai da yawa sun ce India ta yi gaggawar kaiwa Pakistan harin. https://twitter.com/dom_lucre/status/1919866361804706171?t=9WDskLmZiFyzjkOqiS8Tng&s=19 https://twitter.com/dom_lucre/status/1919865357608657377?t=X9pQHu9qyQ6jZXiaEyintg&s=19 https://twitter.com/dom_lucre/status/1919867598478418263?t=EN9LXuWOYGic8JcsFFtojg&s=19 Wasu rahotanni dai sun ce Pakistan din ta sha Alwashin yin ramuwar gayya. Kasar ta Pakistan ta sanar da kulle sararin samaniyar ta na tsawon awanni 48 inda tace tana shirin kai harin ramuwar gayya. Tuni shugaban kasar Amurka, Donald Trump ya bayy...
Arewa kadai ba zata iya sa dan takara ya ci shugaban kasa ba>>Tanko Yakasai

Arewa kadai ba zata iya sa dan takara ya ci shugaban kasa ba>>Tanko Yakasai

Duk Labarai
Babban dan siyasa daga jihar Kano, Alhaji Tanko Yakasai ya bayyana cewa, kuri'ar Arewa kadai ba zata saka dan takara ya ci zaben shugaban kasa ba. Yace hakanan kuri'ar kudu kadai itama ba zata sa mutum ya ci zaben shugaban kasa ba. Yace dole sai yankunan biyu sun hada kai sun kawo dan takara da ya ke da karbuwar da zata sa ya ci zabe, yace kuma dole dan takarar ya zamana yana da kudi. Yace saboda zaben Najeriya dole sai da kudi ake cinsa.
Ƴan Majalisar Wakilai 6 daga jihar Delta sun fice daga PDP zuwa APC

Ƴan Majalisar Wakilai 6 daga jihar Delta sun fice daga PDP zuwa APC

Duk Labarai
Ƴan Majalisar Wakilai 6 daga jihar Delta sun fice daga PDP zuwa APC Ƴan majalisar wakilai 6 daga jihar Delta sun sauya sheka daga jam’iyyar PDP zuwa jam’iyyar APC. Shugaban majalisar, Abbas Tajuddeen ne ya bayyana haka a zaman majalisar na yau Talata bayan ta dawo daga hutu. Yan majalisa shidan da su ka sauya sheka daga PDP zuwa APC sun hada da Victor Nwokolo; Dan majalisa Julius Pondi; Dan majalisa Thomas Ereyitomi; Nicholas Mutu; Okodiko Jonathan da kuma Nnamdi Ezechi. Wasu ‘yan jam’iyyar Labour ma guda biyu daga jihar Enugu su ma sun sauya sheka zuwa jam’iyyar adawa ta PDP, waɗanda su ka hada da Mark Obetta da Dennis Nnamdi. Shugaban majalisar ya ambato ‘yan majalisar na cewa sun sauya sheka ne sakamakon rikicin da ya barke a jam’iyyunsu a jihohinsu da kuma a matakin ...