Friday, December 19
Shadow

Author: Bashir Ahmed

‘Yan gida daya su 5 sun mùtù bayan cin Abinci me guba

‘Yan gida daya su 5 sun mùtù bayan cin Abinci me guba

Duk Labarai
Wasu 'yan gida daya su 5 sun mutu bayan cin abinci me guba a garin Ogidi, dake karamar hukumar Idemili North ta jihar Anambra. Mahaifiyar su ma na can kwance rai hannun Allah a Asibiti. Lamarin ya faru ranar Asabar 3 ga watan Mayu 2025 kuma ya jefa mutanen garin cikin damuwa. Mahaifin yaran Pa Robinson Aghalu dan shekaru 76 wanda tsohon soja ne yace yaran nasa sun fara amai da ciwon ciki ne bayan cin abincin da mahaifiyarsu ta dafa. Su 6 ne suka ci abincin kuma guda 5 sun mutu. Kakakin 'yansandan jihar, SP Tochukwu Ikenga ya tabbatar da faruwar lamarin inda yace sun dauki abincin dan zuwa a yi gwaji.
Ji Dalilin da yasa Hukumar EFCC suka naɗe Gudaji Kazaure zuwa Abuja

Ji Dalilin da yasa Hukumar EFCC suka naɗe Gudaji Kazaure zuwa Abuja

Duk Labarai
Hukumar EFCC a jihar Kano ta kama tsohon ɗan majalisar tarayya Hon. Muhammad Gudaji Kazaure bayan ta gayyaceshi ofishinta kuma ya kai kansa amma daga bisani ta naɗeshi zuwa Abuja. Bayanan da Zuma Times Hausa ta samu sun ce, EFCCin tana neman bayanan wasu kyaututtukan kudade naira miliyan 14 da suka shiga asusun bankin tsohon dan majalisar a wani lokaci a shekarar 2019. Me zaku ce?
Dalibar Da Ta Kammala Digiri Da Sakamako Mafi Daraja A Jami’ar Northwest Dake Kano Ta Koma Tallar Wainar Fulawa Bayan Rashin Samun Aikin Yi

Dalibar Da Ta Kammala Digiri Da Sakamako Mafi Daraja A Jami’ar Northwest Dake Kano Ta Koma Tallar Wainar Fulawa Bayan Rashin Samun Aikin Yi

Duk Labarai
Dalibar Da Ta Kammala Digiri Da Sakamako Mafi Daraja A Jami'ar Northwest Dake Kano Ta Koma Tallar Wainar Fulawa Bayan Rashin Samun Aikin Yi. A yayin jin ta bakin Kwamared Habiba Usman Garkuwa, wadda har ta taba zama shugabar dalibai na jami'ar da ta yi, ta ce ta raba takardun neman aiki adadin da ba za ta iya tunawa ba, amma har yanzu shiru don haka ta yanke shawarar fara soya wainar fulawa da awara. Habiba dai ta fita da sakamako mafi daraja Jami'ar Northwest a shekarar 2024 a fannin ilimin kimiyyar Biology, kamar yadda wanda ya fitar da rahoton, Abdulwahab Said Ahmad ya wallafa a Shafinsa na Facebook.
An kama Barawo bayan da ya saci Keke Napep a masallaci a jihar Naija

An kama Barawo bayan da ya saci Keke Napep a masallaci a jihar Naija

Duk Labarai
Hukumar 'yansandan jihar Naija sun yi nasarar kama wani barawon Keke Napep a jihar. Kakakin 'yansandan jihar, SP Wasiu Abiodun ya tabbatar da faruwar lamarin inda yace lamarin ya farune ranar 5 ga watan April. Sunan Barawon da aka kama Abdulaziz Salisu kuma yayi satar ne yayin sallar Asuba a Dakwa. Yace bayan ya saci Keke Napep din yayi yunkirin kaiwa wani me suna Abubakar Mohammed dan ya sayar masa dashi. Yace ana tsaka da sallah ne Abdulaziz ya fita ya sace Keke Napep din amma sai 'yansanda suka kamashi a gadar Maje inda ya amsa cewa satota yayi.
Likitoci dubu 30 ake dasu a Najeriya

Likitoci dubu 30 ake dasu a Najeriya

Duk Labarai
shugaban kungiyar Likitoci ta Najeriya, Professor Bala Audu ya bayyana cewa, Likitoci dubu 30 ne ake dasu a Najeriya. Ya bayyana hakane a wajan wani taron kungiyar likitocin da ya wakana a Jihar Katsina. Yace a shekaru 5 da suka gabata, Likitoci dubu 15 ne suka bar Najeriya zuwa kasashen Waje. Yace kowane Likita daya yana ganin marasa Lafiya dubu 8. Wanda a ka'ida marasa lafiya dari shida ne ya kamata ace kowane likita na gani.
Ana ta yiwa wani Fasto dariya bayan da yace an masa Wahayin Barcelona ce zata ci Inter Milan amma hakan bai faru ba

Ana ta yiwa wani Fasto dariya bayan da yace an masa Wahayin Barcelona ce zata ci Inter Milan amma hakan bai faru ba

Duk Labarai
Wani fasto na ta shan suka da dariya bayan da yace an masa Wahayin Barcelona ce zata ci wasan Champions League tsakanin ta Inter Milan amma hakan bai faru ba. Ya gayawa mabiyansa cewa PSG da Barcelona ne zasu buga wasan karshe kuma Barcelona ce zata dauki kofin. An dai ta yada Bidiyon wannan ikirari nasa kamin buga wasan. https://www.youtube.com/watch?v=lVc0oSMuyCs Saidai bayan buga wasan, An cire Barcelona. Da yawan kiristoci sun bayyana cewa dama faston karyane.
Wannan matar me suna Valentina Gomez ‘yar kasar Amurka nason a haramta Addinin Musulunci a cikin kasar Amurka

Wannan matar me suna Valentina Gomez ‘yar kasar Amurka nason a haramta Addinin Musulunci a cikin kasar Amurka

Duk Labarai
Wata mata me tsatstsauran ra'ayi me suna Valentina Gomez ta nemi a hana Addinin Islama a cikin jihar Texas. Ta bayyana hakane a yayin da ta je wajan wani taron musulmai ta afka musu da zagi da cin zarafi. Dama dai matar ta yi suna sosai wajan rashin kunya da nuna kiyayya ga Addinin Musulunci. Saidai da yawan Amurkawan basu yadda da wannan ra'ayin nata ba.
Bayan da ya sha matsa a hannun DSS, Shugaban Kungiyar daliban Najeriya a karshe ya yadda ya karyata kansa kan zargin da yawa dan shugabab kasa, Seyi Tinubu cewa ya sa an masa dukan kawo wuka

Bayan da ya sha matsa a hannun DSS, Shugaban Kungiyar daliban Najeriya a karshe ya yadda ya karyata kansa kan zargin da yawa dan shugabab kasa, Seyi Tinubu cewa ya sa an masa dukan kawo wuka

Duk Labarai
{"remix_data":[],"remix_entry_point":"challenges","source_tags":[],"origin":"unknown","total_draw_time":0,"total_draw_actions":0,"layers_used":0,"brushes_used":0,"photos_added":0,"total_editor_actions":{},"tools_used":{},"is_sticker":false,"edited_since_last_sticker_save":false,"containsFTESticker":false} A karshe dai, Shugaban Kungiyar daliban Najeriya, Atiku Abubakar Isah ya fito ya wanke dan shugaban kasa, Seyi Tinubu kan zarge-zargen da ya masa. A baya dai An ga Bidiyon Atiku yana cewa Seyi Tinubu ya masa tayin karbar Naira Miliyan 100 dan ya goyi bayan babansa, Bola Ahmad Tinubu. Yace amma yaki amincewa shine Seyi Tinubun ya dauki nauyin 'yan daba suka lakada masa duka. Saidai bayan wannan zarge-zargen ne hukumar 'yansandan farin kasa, DSS suka kama shugaban daliban, kam...